Bismillahirrahmanirraheem…
Wai meyasa ‘yan dariku suka fi alaka da ‘yan shi’ah? Hakika A aqeedance shi’ah da darika akwai alaka tsakaaninsu.. Toh amma bari muyi dan wata tsokaci, saboda ‘yan’uwa wanda guguwar bid’ah ta debesu su fahimta… A kullum ‘yan dariku sunfi nuna zafinsu akan qiyayyah ga ahlussunnah saboda sunace ahlussunnah suna zagin waliyyansu, ainihin abinda ya janyo gaba mai tsanani kenan tsakanin ahlussunnah da ‘yan darikah. Sannan suna sake fakewa da cewa ahlussunnah suna zagin iyayen annabi, sannan kuma suna rage wa annabi daraja. Toh amma kuma abin mamaki yanda yasa muka gano ashe duk karya sukeyi, su duk babatunsu bawai don ahlussunnah suna rage wa annabi darajah bane, da kuma suna ce iyayen annabi suna wuta.. Shine shigowar mabiya addinin shi’ah.. an tuhume ahlussunnah da zagin waliyyai irinsu shehu tidjani, da su nyass!!!! Aka kashe wassu daga cikin mabiya sunnah saboda wannan abu,. Toh amma shigowar mabiya addinin shi’ah sai suka kafirta waliyyai na ainihi masu register a qur’ani da hadisi, irinsu abubakar da umar da uthman. Da dai sauransu. Suka kuma sake kafirta iyayen annabi(s.a.w)… Toh abin mamaki duk da haka suka samu karbuwa a gurin ‘yan darika. Saboda basu zagin waliyyan boge irinsu tidjani, da nyass… Kaga anan ya bayyana a hakikanin gaskiya ‘yan darika ba suna fada da ahlussunah ne saboda annabi da iyalansa ba. A’a suna fada ne dun ahlussunnah sun taba waliyyan bogi irinsu nyass da tidjani… Domin inda suna fada da ahlussunnah saboda iyayen annabi da sunyi fada da ‘yan addinin shi’ah, saboda ‘yan addinin shi’ah suna da rubutacciyah acikin littafinsu cewa iyayen annabi suna wuta.. Ku duba cikin littafin ‘Mulla muhammad baqir’ wanda akafi sani da allama majlisi.. Littafi mai suna ‘Biharul-anwaar’ wanda wannan littafi tana daga cikin manyan littafin mabiya addinin shi’ah… Kaman yanda in akayi maganar littafin musulmai za’a kawo sahih na bukhari da muslim.
Acikin wanna littafi sukace annabi yace:
“DA ZAN NEMA MUSU GAFARA
DA ABU DALIB ZAN NEMARWA,
SABO DA YAYI MIN ABIN DA
BASU YI MINI BA. TO AMMA
ABDULLAHI DA AMINA DA ABU
DALIB SUNA WANI KWAZAZZABO, DAGA
CIKIN.KWAZAZZABUN JAHANNAMA” Toh kunji fa… Ina ‘yan darika masu babatu cewa ahlussunnah suna zagin iyayen annabi? A wani littafin ahlussunnah ne kukaga ya zagi iyayen annabi? Wato a hakikanin gaskiya an ribaci jahilcin mabiya ne aka cusa musu irin wannan aqeedar. Domin da yawa zakaji mabiya suna ce ahlussunnah suna zagin iyayen annabi, amma inka tambayesu a’ina suka gani bazasu iya bada bayaani ba… Wannan zargine wanda bata da tushe… Saboda haka mukeso mabiya a zurfafa bincike domin kada ku kama gaaba da wasu gabar da kuma baku da dalilin yinta…. Sannan shin kunyarda da ‘yan shi’ah, duk da suna zagin sahabbai? Amma kunki ‘yan sunnah saboda suna zagin nyass da tijjani? Toh anan su tijjani da nyass sunfi sahabbai ne? Haba ‘yan darika ku kula kuyi nazari kada a cusaku cikin shirme da rudu… Allah yasa mudace, Allah ka nuna mana gaskiya ka bamu daman binta, ka nuna mana karya ka bamu daman kauce mata… Yaa Allah ka shiryar damu tafarki madaidaiciya. Wa’innan ‘yan’uwa namu ka shiryar dasu da mu baki daya… Wassalaam…
Leave a Reply to ANAS HARKACancel reply