Takaitattun Tarihin zantukan Sufayen Farko

·

·

Domin neman ƙarin bayani danna nan

Bismillahirrahmanirraheem.
Shin wai masu ikrarin sufanci a zamaninmu na yanzu shin sufayen ne da gaske ko kuma ‘yan cuwa cuwa ne? Ya dace ‘yan uwa mu fahimci abinda mukeyi kada mudinga ruduwa da shirme mu daukeshi a matsayin addini. Addini na littafin Allah addini na hadisan manzon Allah(s.a.w). Zan hakaito mana wasu daga cikin kalamai na sufaye na farko domin mu gwada wannan kalamai da kuma halin da wasu masu karyar sufanci suke ciki.
Shin da farko a takaice meye sufanci da ginu akai? Ta ginu ne kan gudun duniya, da bautar Allah. sufi yakan kaurace wa jama’a ya koma kan dutse yayi zamansa yayi ta bautar Allah. Haka abin ya fara yana tafiya. Kafin tafiyar tazo ta samu matsalar da ‘yan bid’ah suka ruda ta. Duk da dai ita sufancin bata da asali a addini, kuma malamai sunyi bayani akai. Amma zan rubuto kalaman ne saboda mabiya sugane ainihin sufanci na da din.
Da Farko ga bayanin Da junaid yayi, wanda in ana magananan sufanci ne dole a sanya su aciki. Domin su kusoshi ne.
قال جنيد رحمه الله: طريقتنا هاذا مقيد بالكتاب والسنة. من لم يحفظ الكتاب ولم يحفظ الحديث فلا يقربن طريقتنا.
Junaid Allah ya gafarta masa yace: WANNAN DARIKA TAMU AN KAYYADE TANE AKAN LITTAFIN ALLAH DA KUMA HADISIN MANZON ALLAH, DUK WANDA BAI KIYAYE LITTAFIN ALLAH BA, KUMA BAI KIYAYE HADISAN MANZON ALLAH BA TOH KADA YA KUSANCI DARIKARMU….
Sannan Ga kuma abinda Sahl al tustari yake cewa:
أصول طريقتنا خمسة.
1.التزام بالكتاب والسنة.
2.الإقتداء بنبي الأمة.
3.أكل الحلال.
4.العفو عن من ظلمك.
5.لزوم التوبة.
Yace: asalin hanyar mu Guda biyar ne:
1.ka lazumci littafin Allah da sunnar annabi(s.a.w).
Toh dun Allah yanzu ina masu kiran kansu sufaye ina sunnar annabi? Sai dai abaki. Abinda ake nufi da lazumta shine: ya zama koda yaushe kana mai aikatashi, da zarar kaji ance annabi yace kaza, ko yayi kaza, kaima ka aikata shi. Ance annabi na son aswaki, kaima kaso aswaki, ance annabi na barin gemu, kaima bar gemu, ance annabi na sallan dare, kaima tashi kayi, ance annabi na azumin litini da alhamis,kaima daure kayi. Ance annabi baya barin tufafinsa yaja kasa, kaima dage naka, irin wa’innan su ake kira sunnah, da zarar ankawo maka hadisi inagatacce, ta dace da son zuciyarka bata dace ba karbeta. Amma
rawa, kida da fada a baki, ba ita ke nuna bin sunnar annabi ba. Wani malami yake cewa:
ومن محبته صلى الله عليه وسلم. انتصار سنته.
Yace yana daga cikin son manzon Allah(s.a.w) taimakon sunnarsa… Ina masu kururuwan son annabi? Ba yiwa annabi waka da rawa shi ke nuna son annabi ba. A’a, ka taimaki sunnarsa, ka yada addinin da yazo dashi. Ka bi duk abinda yace ka kaurace wa abinda yayi hani akai….wannan itace hakikanin son annabi, amma bawai fada da baki ba.
2.na biyu yace, yin koyi da Annabi(s.a.w)..
Ya zamto duk abinda zakayi kana koyi da annabi ne. Kafin ka zama sufi na gaskiya sai ya zamto duk abinda zakayi kana koyi ne da annabi(s.a.w) ba zaka kirkiri wata kalar ibadah dabam ba irin ta annabi ba, ba zakayi sallah ba irin ta annabi ba. Ba zakayi zikiri ba irin ta annabi ba.
3.na uku yace: cin halal. Duk wani sufi na gaskiya zakaga ya toge kan cin halal. Babu ruwanshi da haram..
4.asali na hudu yace, yafiya ga wanda ya zalunce ka.. Duk sufi na gaske babu ruwanshi da hayaniya, duk abinda aka mishi yafewa yakeyi. Ba zai zalunceka ba, kuma inka zalunce shi sai ya yafe.
5. Sai na biyar yace: lazumtar tuba.. Duk sufi zaka sameshi a kullum mai lazumtar tuba ne… Mai kankan da kai zuwa ga Allah…
Wa’innan sune kalaman sahl al tusturi. Dun Allah ‘yan’uwa ku kula da irin wannan zantuka na hamshakan malaman sufanci na gaske… Idan aka dauki wa’innan ka’idoji aka sanya akan masu ikrarin sufanci na yanzu za’a samu sufi ko guda daya? Ko daya babu. Sannan meyasa basu fitar da irin wannan kalaman suna tallata wa mabiyansu? Dun Allah ga aiki na baiwa duk wani dan’uwa mabiyin darikah..
1. Ya dauki wannan ka’idojin wanda kusoshin sufanci suka fada, ya daurashi kan shehinsa, ko malaminsa, yaga inba shehinsa ko malaminsa na kan ramin halaka ba, yanzu dun Allah suwaye masu fada da kitaab wa sunnah? ‘yan dariku, gashi kuma sahl ya fara kawo cewa darikarsu tana rataye ne da kitaab wa sunnah.
2. Na biyu.. Meyasa ba’a bude majalisi na littafai wanda sufayen zamani suka rubuta? Irin littafin jawaahiru ma’ani, Meyasa? Shin sun qunshi gaskiya kuwa? Su duba duk wani malamin sunnah in ya buga littafi ana bude majalisi a karanta abinda ya rubuta.. Amma ku tambayi kanku meyasa ba’a karanta naku?….
Daga karshe duk maison gane hakikanin tasawwufanci, to ya binciki wallafe wallafen wa’innan bayin Allah. Irinsu sahl al tusturi, ibrahim ibn adham, irinsu junaid. Da abdulkadir jailani. Domin shima abdulkadir jailani ahlussunnah ne. Duk masu maqalewa dashi a tafarkin darika karya sukeyi… ‘yan’uwa matasa mabiya darikah. Wallahi inkunason gaskiya ku binciki littafan wa’innan maluman da kuma tarihinsu, wa’inda sune jagorori a harkar sufanci,kusha mamaki. Wallahi sai kun gudu kunbar wannan shirme da kukeyi da sunan addini… Zaku tabbatar an rudeku.. Mu mun karanci sufancin zamani da aqeedunsu, sai muka gujesu. Kaima dan’uwa ka karanci aqeedar ahlussunnah mana a rubuce muga ko. zaka kisu? Kadaina amfani da malam wane yace, ko wane ya aikata kaza. A’a karanta a rubuce ka fahimta, wannan itace hakikanin gaskiya.ina aka samu wai malami ya zauna a gida bayi da aikin komai wai sai roka wa mutane Allah. Shin wannan abu na da asali a addini? Malam baka fita jihadi, baka fita wa’azi, kai kenan kullum ka tsubbace kanka wuri daya? Shin haka annabi ya rayu ta wannan hanya? Ina aka samu raba wa mutane darika? Shin akwai wani nassi da ya tabbatar da haka? Ina aka samu kirkirar bid’ah da sunan mai kyau? Yaa dace jama’ah ayi lura, yanzu lokaci ya wuce da za’ayi ta mana nuku nuku. Komai ya fito fili mun gane. Maison gaskiya yaci gaba da bincike Allah zai nuna masa.. Jama’a ayi hakuri in na tsawaita…. Allah yasa mugane, Allah ka shiryar damu Hanya madaidaiciya. Wanda kuma ranshi ya baci da zantuka na, yayi hakuri. Ni inayi ne saboda kauna da nakeyi wa ‘yan’uwa wanda suka kauce wa hanya. Wassalaamu alaikum wa rahmatullah.

31 responses to “Takaitattun Tarihin zantukan Sufayen Farko”
  1. Yusufshamza Avatar

    Hmm ashe kun suma gane gaskiya kun gane sufaye bayin Allah ne na gaskiya. Ka fadamun acikin wadannan sharuda wanne ne ba’a cika ba. don karin bayani ka nemi ne a email

  2. A.A Maradun Avatar
    A.A Maradun

    AMMA SUFANCIN DA AKE YI YANZU TSABAR BIDIAH DA SHIRKA KE CIKINSA HAR SUN KAI GA FITOWA FILI SUNA BADA ULUHIYYA GA SHEHUNNANSU. ALLAH YA KIYASHE MU ! AMIIN.

    1. Yusufshamza Avatar

      Ashe kuwa ibn taimiyya shine babban mushriki idan baka san waye ibn taimiyya je ka duba littafin ibn Kayyim

    2. Nasir Avatar
      Nasir

      Bawan Allah A Dinga Yin Adalci, Yanzu Tsakanin Mu Da Ku Suwane Suke Shirka,kuma Ka Fadan Abu Daya Ake Na Shirka.

  3. ANAS HARKA Avatar
    ANAS HARKA

    GASKIYA BIN TAIMIYYA YAYAI GASKIYA WAJAN SANAR DAMU GASKIYAR SUFAYI AIYANXU SUFANCE KARYA NE DA DAFFARA DA WAKOKIN BANXA DA HOFEE

  4. Ibn Uwais Avatar
    Ibn Uwais

    Kusani ku Yan Izalatussunnah wa Iqamatul bid’a, Duk abinda ya Inganta a Sufanci Sunnar Annabine: Bada Dariqa yabo ga Annabi, Kida, Rawan shauqin Sunan Allah dana Manzonsa da sauransu, Inda mai Shakku Ina jiransa! Kuma Taswauwuf Sunnane daga Annabi.

  5. ILIYASU IBN ALIYU Avatar
    ILIYASU IBN ALIYU

    Assalamu alaikum warahamatullahi ta.ala wabarka tuhu Allahumma salli ala muhammad wa.ala ali muhammad kama sallaita ala ibrahima wa.ala ali ibrhm fil alamina innaka hamidl majid. bayan gaisuwa irin tamu ta addinin musulunci da salati ga fiyayyan halita Annabi S.W.A.
    Dafarko dan uwa mai ikrarin wai ka fadada bincike to awoka domin kuwa idan kana tunanin kayi sammako to wani a hanyar ya kwana.zantukan da ka ruwaito akwai alamar rashin nazari da kuma rashin lissafi,Ga amsar tambayoyinka da izinin Allah .
    1.shehinnan darikah kowa ya san sune mahaddata Alkur’ani aduk inda suke ko kaima shaida ne in zaka fadi tsakaninka da Allah kai bugu da kari ma a unguwarku wallahi nasan indai akwai yan dariku baxa arasa mahaddata ba.toh ya xa.ayi wanda yayi haddar Alkur.ani ya haddatar da wasu yakuma san hadisai Amma ka fito a idon duniya ba kunya ba tsoron Allah kai masu karya?
    2.karyata sidi abdulkadir jilani da kayi akan darikarsa kaji kunya walh. Darikar da duniya ta san da ita amma kake kokarin kawo wasu zantukan da duk wani mai ilimi da hankali xaimaka dariya a daukeka wawa mara tunani.
    3.toh ai dama kune jahilai marasa ilimi duk wanda yasan kur.ani yasan hadisi ahlussunnane, darikun sufaye tundaka farko har izuwa karshe masana ilimoma ne kai harma bayin Allah masu bin tafarkinsu.
    GA TAMBAYOYI KU AMSA MANA
    1.Me yasa aka kirkiri iZALA ko kuma akawo mana hadisin da ya tabbatar mana manxon S.A.W yace xa ta xo bayan hijiransa da shekara Dubu da dari hudu ??
    2.mene asalin Takubban nan guda biyu da itace nacikin logon ku??

  6. Nura senior Avatar
    Nura senior

    Slm kai bakasan inda ilmin addin ya yiba ma balle ka bishi ai malaman da kace suna zama suna tsubbu ba sufaye bane da kayi karatu da kasan inda almajiran na khaulaha suke cikakkun sufaye tambaya ka gayamin gidan malamin kungiya guda daya da ake karatun alqu rani dare da rana kuma idan ya mutu yana da halifa da ma Allah ya gaya manaهوالأبتر‎ ‎اناشانعك ‏‎

  7. Idrismuhammad Avatar
    Idrismuhammad

    Allah mai iko gagaskiya ga rashin ganeta.
    Wallahi masu qarya dasunna ayau kunji kunya iya matuqa tun’anan duniya ballantana idan munje …..
    Wanda yabata lokacinsa wajan gwama gaskiya qarya, dasan zuciya yatabe kuma ya wulaqanta. Inayin jawabina adunqulene ba mai ganewa sai fasihi.
    Babbar qarya dayayi itace Sheikh Abdulqadir jiyyali Bawahabiyene domin yace yandariqa suna da’awar nasune amma ahlussunnane kuma ayau dakaji ba’izale yakiraka ahlssnna to ma’anarsa kai bawahabiyene!.
    Allahumma ajirna min khaidil wahaabiyya. Ameen S.A

  8. Shehu kasimu Avatar
    Shehu kasimu

    ALLAH! YAJIKAN MALAM DA RAHAMA YAKUMA SAKAWA MALAM DA ALKHAIRI WURIN TSAYAWA TSAYIN DAKA GANIN AL:UMMAN MUSULMAI SUNSA KAUNAR MANZON ALLAH(S A W) AZUKATANSU DA KUMA KOYI DA AIYIKA IRIN NA MANZON ALLAH(SAW)

  9. […] Takaitattun Tarihin zantukan Sufayen Farko. […]

  10. Aliyul harazimi Avatar

    Allah yai jagora

  11. Auwal shehu Avatar

    ASHE KUFARA GANE GASKIYA DOMI A MAGANAR DAKA KAWO KACE SUFAYE AN SANSU DA BAUTAR (ALLAH) DASANNU ZAKU GANE GASKIYA KUMA DUK SUNNAR DAKA FADA YAKAMATA AYI WACECE MALAMAN KU BASUZO SUKA RUSKI MALAMMU SUNAYIBA ADAY JE AKARO ILIMI IYALIN ZULKUWAY SARA.

  12. UMAR ABDULLAHI Avatar

    allah ya ka remu daga sharrin kagaggun kungiyoyin addinin musulunci,wanda yake ka garsu bidi,a ce abarki,domin bawata ayah ko hadisin manzon allah(saw)da yace idan kabi kagaggun kungiyoyin katsira.sai iya fadar sunnah abaki aka sa aikatawa afadi dubu akasa yin goma. allah ya kiyaye amun.sannan kuma ga muguwar hassada ga manyan bayin allah wa’inda yayar da dasu harya basu karama.abun tambaya anan shine shin wa innan mutane yanbidi’a ne amma allah ya basu karama baiba wa in da suke ikirarin su ahalul sunnabane?daga farouk

  13. yahaya ibrahim Avatar
    yahaya ibrahim

    Allah kajikan shehu aliyu harazimi

    1. Abubakar Harazumi Avatar

      Ameeeen

  14. nura zamani Avatar

    jahilan yan izala wadan da basa laifi

  15. nura zamani Avatar

    wawaye wadan da ke da tsoron haduwa da shark abduljabar sai dai ashiga internet ayi kuce ayi sharri aji karya wawayen jahilai marasa tunani wai salap ko ahlilsunna amma bata annabiba kokuuwa izala daga nura muhd banizumbu dandi local govt kebbi state

    1. yahaha Avatar
      yahaha

      Allah yashiryemu zagidai dabiar yan wutane

  16. Abubakar Umar Avatar
    Abubakar Umar

    Alhamdulillah tunda kun yarda Shehu Abdulkadir jilani ahlul Sunnah ne, to abin da yayi Shehu Abdulkadir,imumu tustari,imamu busari,ibn arabi,imamu junaidu, to Ku sanifa shi yai Shehu Tijjani (RTA)
    Allah ya karamana son sufaye ya bar da su

  17. Ibraheem yahaya abdullahi Avatar
    Ibraheem yahaya abdullahi

    Allah ta doramu akan hanya madedeciya ameen

  18. Ummar babajo Avatar

    Wai Allah! Jahilci mugun ciwo, kai da kaga wannan kalaman kasan cike suke da jahilci, toh idan ya zamana su malaman namu ba sufaye bane na hakika toh a cikin irin malaman naku ka gayamana wake da irin haalayen sufancin, ko kuwa su ba bayin Allah bane, jakin banza jahili kawai

  19. Attahir Avatar
    Attahir

    izala damfara cin kudin makamai

  20. Rabiu Abubakar Avatar

    Allah shiryar damu hanya madaidai ciya

  21. baba musa Avatar
    baba musa

    Allah dai yasa mudace.

  22. Muhammad Adam Avatar
    Muhammad Adam

    wannan zancen banzane wallahi ba ataba jahilai a duniya ba irin Izala kuma ba za akaraba.June kuyi karatu ba jayayya ba.gaskiya gaskiyace Katya kuma karayace………..Allah shiryemu shirin addinin musulunci da sunnar annabikaSAW……….

  23. yahaha Avatar
    yahaha

    Allah kashiryemu zagidai dabi’ar yan wutane

  24. Zancan Banzan Wofi Karya Kuke

  25. Akibu m yahuza na malan kawu Avatar
    Akibu m yahuza na malan kawu

    Tabbas malan ka nunama duniya cewa members ne kuke nema.

  26. Muhammed Musa Avatar

    Salamu Alaikum Yan Uwa Musulmai Mabiya darika.Allahumma Salli Ala Sayyidina Muhammadu Alfatihi Lima Ugulika Wal-khatimi Lima Sabaka Nasiril Hakki- Bilhak Wal Hadi Ila Siradikal Mustakim Wa’alaa Alihi Hakal-kadrihi Wamik-darihil Azeem.Adadi Nurika Ya Allah.; A Haka Ake cewa Musulmi Dan Uwan Musulmi kuna mana Bakin Cikin Ladan dazamu Samu Dan Ku Bazakuyiba? waifa Yarene Akayi Mutum Baiji Yaren Ba Zai Iya Fassarata?Bazai Iyaba,sai Dai Yaje Wurin Wanda Yai Yaren Yai Ladabi Ya Kaskantar Da Kansa Idan Har yanaso Ya Iya.Yan Izala kuje gurin yan Darika Ayi Maku Tarbiya Ku Zama Sufaye.Ko Bakuso Ku Kusan Ci Allah Ne?,sai Dai Duniya?Kankanuwa Kuma Kararra. Ku Zama Musulman Kirki Manaa.

  27. darikar tijjaniya darikace ta sufaye wacce take nuni da soyayya da istigfari da hailala da salati ga annabi(saw)domin Allah ne yai umarni da hakan innallaha wamala’ikatihi yu salluna alannabiyi …. ba wai hanya bace ta nuna son zuciya ba ko bada ko haramta wa abu ba nafsi ba hadisi imam malik yace duk wanda aka tambaye shi to ya tabbata yana tsakanin wuta da aljanna ne sai yasan yanda zai kubutar da kansa ta hanyar nazari amma ka duba malaman mu yanzu har anmai da fawa abar neman sund sayyadina abubalar umar,usman,ali sune manyan sahabban annabi kuma idan ilmine da fahimtar addini baka kaisuba amma duk yayin da akazo musu da tambaya sai dayansu ya kirawo yan uwansu sahabbai domin tattaunawa akan tambaya. kuma watarana bawani mutum daga maghrib yazo da tambaya gun imam malik akan wanani mas’ala sai imam malik yace yaje yadawo domin yin nazari akai sai wa shegari mutuminnan ya dawo sai imam malik yace wlh ban sani ba. amma ni ban san sanda addini ya koma zauran tattanawaba batare da batare da’aya da hadisi

Leave a Reply to Abubakar UmarCancel reply

Latest updates
Categories