WASU DAGA CIKIN HAKKOKIN
MIJI AKAN MATARSA.
1-Soyayya ta gaskiya.
2-Tsare Amana Miji.
3-Tausasawa miji da wasa da
dariya dashi.
4-Tsare sirrin miji.
5-Kada ta fita daga gidansa sai da
izininsa.
6-Baza tayi azumin nafila ba sai da
izininsa.
7-Ta yarda ya sadu da ita duk
lokacin da yake bukata, dan
Annabi Mai tsira aminci yace duk
matar da taki mijinta ya sadu da ita
a duk lokacin da yake so, to
Mala’iku zasuyi ta la’antar ta
bazasu su daina ba har sai lokacin
da ta yarda da shi. (BUKHARI/
MUSLIM).
8-Ta saurari mijinta kuma tayi
masa biyayya matukar ba aikin laifi
ya umurceta dayi ba.
9-Mace ta nisanci raina abin da
mijinta ya bata, domin Annabi
muhammad mai tsira aminci yace
“Mata zasu shiga wuta ne saboda
kafurce wa mazajensu, wato raina
alherin miji” (BUKHARI/MUSLIM)
10-Kada mace ta cutar da mijinta
da magana ko da aiki.
11-Mace tayi ado da kwalliya wa
mijinta, saboda Annabi mai tsira da
aminci yace “Allah kyakkyawa ne,
kuma yana son kyakkyawan
abubuwa, (IMAM MUSLIM YA
RUWAITO)
12-Mace ta tsare dukiyar mijinta
dana ‘ya’yansa harma dana
gidansa, dan Annabi mai tsira da
aminci yace “Mace mai kiwo ce a
gidanta, za’a tambayeta abin da ta
kiwata.
13-Mace tayi gaggawan baiwa
mijinta hakuri a duk lokacin da
taga yayi fushi, Tace masa, dan
Allah kayi hakuri, bansan abin da
nayi zai bata maka rai ba, ka yafe
mini dan girman Allah.
14-Mace tayiwa mijinta dukkan irin
aikin da ake bukata ayishi a gida.
15-Mace ta kyautata halayenta ga
iyalan mijinta.
16-Mace kada tayi abokantaka da
mugayen kawaye, sai su hallakar
dake baki sani ba.
17-Mace ta zama mai tausayawa
mijinta, kamar yadda uwa take
tausayin ‘Danta.
18-Mace ta zama mai Biyayya ga
mijinta.
19-Mace ta zama Abokiyar rayuwa
ga mijinta.
20-Mace ta kusanci dukkan abin
da mijinta yake so.
21-Mace ta nisanci dukkan abin da
mijinta yake ki
22-Kiyi murmushi a duk sanda
mijinki ya kalleki.
23-Kiyi masa addu’a a duk lokacin
da zai fita, kice adawo lafiya Allah
ya bada sa’a.
24-Kiyi masa addu’a kuma a duk
lokacin da bakya ganinsa bayan
bayanan.
25-Idan mijinki ya dawo ki karbi
abin hannunsa, tare da yi masa
sannu da zuwa, dan girmama shi.
26- A duk samda zakiyi magana da
mijinki ki gaya masa magana mai
dadi, mai tabshi, kada ki daga
muryanki akan nasa, kuma kada ki
masa tsawa har ki harare shi.
27-Ki zama cikin tsabta da kamshi
mai dadi duk lokacin da kuke tare.
28-Ki sanya hijabi a duk lokacin da
kuke tare da wadanda ba
muharramanki ba.
29-Kisa lokaci idonki, ki kuma
shafa jan baki, kuma ki shafa
turare, amma sai kuna tare dashi a
gida dan mace bata shafa turare
ko janbaki ta fita anguwa dashi.
30-Ki kaskantar da kai dan biyayya
a gare shi.
31-Ki san lokacin da yake dawowa
dan kada ya sameki a cikin
kazanta, ki kuma san lokacin cin
abincin sa dan ki tanada ba sai
yazo yana nema ba.
32-Bayan kin gama masa komi ki
tambaye shi ko yana da wata
bukata a gareki, dan mi biya masa
ita.
33-Kar ki nuna murnan ki idan
wata hasara ta same shi, ki nuna
masa kamar kece kika yi hasarsar.
34-hakanan kiyi murna da duk
wani alherin daya samu.
35-Ki zama kamar matan
sahabbai, yadda sukewa
mazajensu. Idan miji zai fita sai
suce a dawo lafiya, kar ka kawo
mana haram zamu iya hakuri da
yunwar duniya, amma baza mu iya
hakuri da azaba ba gobe lahira. In
ya dawo kuma su karbeshi, suyi
Masa sannu da zuwa suce masa
yau wace aya ne ta sauka kuma
wane hadithi manzon Allah mai
tsira da aminci ya fada.
In dare yayi kuma sai tayi wanka,
ta zabi tufan da yafi kyau ta
rangada ado, ta fuskanci mijinta
tana tana fara’a tana murmushi,
tana ce masa kana da wata
bukatane gareni? In kana da
bukata ka biya.
To ya ke ‘yar uwa musulma, idan
kina son tsira duniya da lahira ki
kiyaye harkokin kuma kiyi aiki
dasuidan ba haka kuma ki tuna
ranar mutuwa da za’a saki cikin
kabari ba taburma, ba katifa, ba
gado, ba window, ba kofa, bama
wata iska da zata sameki, daga ke
sai halinki. A cikin kabari a doka
miki tukwane a kanki a saka
itatuwa a tattare, asa ganye a
doddara, a kwaba kasa a lillike
sannan a kawo sauran kasan data
rage a rufe kabarin da kike ciki
Innalillahi wa inna ilaihi ra’jiun.
Idan kuma kina son Allah Ta’ala ya
yalwata, kuma ya haskaka, kuma
kabarinki ya zama dausayin
Aljannah to ki kiyaye wadannan
harkokin mijinki a kanki domin
Annabi mai tsira da aminci yace da
wata mace, “Mijinki Aljannarki ko
wutarki, ki duba kiga yaya
matsayinki a wurin mijinki, kin tsare
hakkokin sa ko baki tsare ba, idan
kin tsare to ya zama aljannar ki
kenan, (IMAM AHMAD YA
RUWAITO KUMA ADAWI NE YA
INGANTA HADITH DIN).
Allah ya bamu ikon yin daidai a
dukkan al’amurran mu.
Leave a Reply to Muhammad Aminu BunzaCancel reply