WASU MAGANGANU DA YA KAMATA A RUBUTA SU DA ZINARI(Dr Ibrashim Jalo Jalingo)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

(1) Shaikhul Islam Ibnu Taimiyyah
ya ce cikin Majmuu’ul Fataawa
6/505:-
(( ﻭﺍﻟﺨﻴﺮ ﻛﻞ ﺍﻟﺨﻴﺮ ﻓﻲ ﺍﺗﺒﺎﻉ ﺍﻟﺴﻠﻒ ﺍﻟﺼﺎﻟﺢ
ﻭﺍﻻﺳﺘﻜﺜﺎﺭ ﻣﻦ ﻣﻌﺮﻓﺔ ﺣﺪﻳﺚ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ
ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻭﺍﻟﻔﻘﻪ ﻓﻴﻪ ﻭﺍﻻﻋﺘﺼﺎﻡ ﺑﺤﺒﻞ ﺍﻟﻠﻪ
ﻭﻣﻼﺯﻣﺔ ﻣﺎ ﻳﺪﻋﻮ ﺍﻟﻰ ﺍﻟﺠﻤﺎﻋﺔ ﻭﺍﻷﻟﻔﺔ ﻭﻣﺠﺎﻧﺒﺔ
ﻣﺎ ﻳﺪﻋﻮ ﺍﻟﻰ ﺍﻟﺨﻼﻑ ﻭﺍﻟﻔﺮﻗﺔ ﺍﻻ ﺍﻥ ﻳﻜﻮﻥ ﺃﻣﺮﺍ
ﺑﻴﻨﺎ ﻗﺪ ﺍﻣﺮ ﺍﻟﻠﻪ ﻭﺭﺳﻮﻟﻪ ﻓﻴﻪ ﺑﺄﻣﺮ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﺠﺎﻧﺒﺔ،
ﻓﻌﻠﻰ ﺍﻟﺮﺃﺱ ﻭﺍﻟﻌﻴﻦ.(( ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma’ana: ((Sannan alheri kuma
dukkan alheri yana cikin bin
magabata na gari, da kuma
yawaita ilmin hadithin Manzon
Allah mai tsira da amincin Allah, da
kyakkyawar fahimta cikinsa, da yin
riko da igiyar Allah, da lazimtar
abin da ke kira zuwa ga jama’a da
hadin kai, da nisantar abin da ke
kira zuwa ga sabani da rarraba, sai
fa abin da ya kasance al’amari ne
bayyananne da tabbas Allah da
manzonSa ne suka yi umurni
cikinsa da wani umurni na a
nisanta, to wannan kam biyayya
sau da kafa)). Intaha.
(2) Alhaafiz Ibnu Rajab ya ce cikin
littafinsa Alhikamul Jadiiratu Bil
Izaa’ah shafi na 12:-
(( ﻓﺎﻟﻮﺍﺟﺐ ﻋﻠﻰ ﻛﻞ ﻣﻦ ﺑﻠﻐﻪ ﺍﻣﺮ ﺍﻟﺮﺳﻮﻝ ﺻﻠﻰ
ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻭﻋﺮﻓﻪ ﺍﻥ ﻳﺒﻴﻨﻪ ﻟﻼﻣﺔ ﻭﻳﻨﺼﺢ ﻟﻬﻢ
ﻭﻳﺄﻣﺮﻫﻢ ﺑﺎﺗﺒﺎﻉ ﺃﻣﺮﻩ ﻭﺍﻥ ﺧﺎﻟﻒ ﺫﻟﻚ ﺭﺃﻱ ﻋﻈﻴﻢ
ﻣﻦ ﺍﻻﻣﺔ، ﻓﺎﻥ ﺍﻣﺮ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ
ﻭﺳﻠﻢ ﺍﺣﻖ ﺍﻥ ﻳﻌﻈﻢ ﻭﻳﻘﺘﺪﻯ ﺑﻪ ﻣﻦ ﺭﺃﻱ ﺍﻱ ﻣﻌﻈﻢ
ﻗﺪ ﺧﺎﻟﻒ ﺃﻣﺮﻩ ﻓﻲ ﺑﻌﺾ ﺍﻻﺷﻴﺎﺀ ﺧﻄﺎ، ﻭﻣﻦ ﻫﻨﺎ
ﺭﺩ ﺍﻟﺼﺤﺎﺑﺔ ﻭﻣﻦ ﺑﻌﺪﻫﻢ ﻋﻠﻰ ﻛﻞ ﻣﺨﺎﻟﻒ ﺳﻨﺔ
ﺻﺤﻴﺤﺔ، ﻭﺭﺑﻤﺎ ﺍﻏﻠﻈﻮﺍ ﻓﻲ ﺍﻟﺮﺩ ﻻ ﺑﻐﻀﺎ ﻟﻪ، ﺑﻞ
ﻫﻮ ﻣﺤﺒﻮﺏ ﻋﻨﺪﻫﻢ ﻣﻌﻈﻢ ﻓﻲ ﻧﻔﻮﺳﻬﻢ، ﻭﻟﻜﻦ
ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﺣﺐ ﺍﻟﻴﻬﻢ، ﻭﺃﻣﺮﻩ ﻓﻮﻕ ﺍﻣﺮ ﻛﻞ
ﻣﺨﻠﻮﻕ، ﻓﺈﺫﺍ ﺗﻌﺎﺭﺽ ﺍﻣﺮ ﺍﻟﺮﺳﻮﻝ ﻭﺃﻣﺮ ﻏﻴﺮﻩ
ﻓﺄﻣﺮ ﺍﻟﺮﺳﻮﻝ ﺍﻭﻟﻰ ﺍﻥ ﻳﻘﺪﻡ ﻭﻳﺘﺒﻊ.(( ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma’ana: ((Abin da ke wajibi a kan
dukkan wanda umurnin manzon
Allah mai tsira da amincin Allah ya
same shi kuma ya san shi to ya
bayyana shi ga Al’umma, ya musu
nasiha, ya umurce su da bin
umurninsa koda kuwa hakan ya
saba wa ra’ayin wani babba cikin
Al’umma, domin umurnin Manzon
Allah shi ya fi cancanta da a
girmama kuma a yi koyi da shi a
kan ra’ayin wani wanda ake
girmamawa da ya saba wa
umurninsa cikin sashin wasu
abubuwa a bisa kure, daga ma nan
ne Sahabbai da wadanda ke
bayansu suke yin raddi a kan
dukkan mai saba wa Sunnah
Sahihiya, sau da dama ma sukan
yi kaushi cikin raddin, ba kuma
saboda nuna kiyayya gare shi ba,
a’a yana nan abin so a gare su
kuma abin girmamawa a cikin
rayukansu, to sai dai manzon Allah
shi ya fi soyuwa a wurin su, kuma
umurninsa yana sama da umurnin
ko wace halitta, saboda haka idan
umurnin Manzo ya yi karo da
umurnin waninsa, umurnin Manzon
ne ya fi cancanta da a gabatar
kuma a bi)). Intaha.
(3) Shehu Uthmanu Dan Fodiyo ya
ce cikin littafinsa Ihyaa’us Sunnah
Wa Ikhmaadul Bid’ah shafi na 8:-(( ﻗﺪ ﺍﻧﻌﻘﺪ ﺍﻹﺟﻤﺎﻉ ﻋﻠﻰ ﺍﻥ ﺁﺭﺍﺀ ﺍﻟﻤﺠﺘﻬﺪﻳﻦ ﻛﻠﻬﺎ
ﻣﺴﺎﻟﻚ ﺍﻟﻰ ﺍﻟﺠﻨﺔ ﻭﻃﺮﻕ ﺍﻟﻰ ﺍﻟﺨﻴﺮﺍﺕ، ﻓﻤﻦ ﺳﻠﻚ
ﻣﻨﻬﺎ ﻃﺮﻳﻘﺎ ﻭﺻﻠﻪ ﺍﻟﻰ ﻣﺎ ﻭﺻﻠﻮﺍ ﺍﻟﻴﻪ ﺣﻘﺎ، ﻭﻣﻦ
ﻋﺪﻝ ﻋﻨﻪ ﻗﻴﻞ ﻟﻪ ﺳﺤﻘﺎ، ﻭﻳﺠﻮﺯ ﺗﻘﻠﻴﺪﻫﻢ ﻓﻲ ﻛﻞ
ﺭﺃﻱ ﺍﻻ ﻣﺎ ﺧﺎﻟﻒ ﻧﺺ ﺍﻟﻘﺮﺍﻥ ﺍﻭ ﻧﺺ ﺍﻟﺤﺪﻳﺚ ﺍﻭ
ﺍﻟﻘﻮﺍﻋﺪ ﺍﻭ ﺍﻹﺟﻤﺎﻉ ﺍﻭ ﺍﻟﻘﻴﺎﺱ ﺍﻟﺠﻠﻲ ﻓﺎﻓﻬﻢ .))
ﺃﻧﻬﻰ.
Ma’ana: ((Hakika Ijmaa’i ya kullu a
kan cewa lalle ra’ayoyin Mujtahidai
dukkansu hanyoyi ne zuwa
Aljannah, kuma hanyoyi ne zuwa
alkhairai, wanda duk ya bi wata
hanya daga cikinsu to tabbas za ta
kai shi zuwa inda suka kai, wanda
kuma ya karkata ga barin hakan
sai a ce da shi tir. Kuma yin koyi da
su na halatta cikin dukkan wani
ra’ayi, sai dai abin da ya saba wa
nassin Alkur’ani, ko nassin Hadithi,
ko Ka’idodi, ko Ijmaa’i, ko
Bayyanannen Kiyasi, ka fahimta)).
Intaha.
Muna rokon Allah Madaukakin
Sarki da Ya cusa mana son
sahihiyar Sunnah da kuma son yin
aiki da ita cikin dukkan wani abu
na Aqiidah, ko Ibaadah, ko
Mu’aamalah. Ameen

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories