JESUS AND RAMADAN

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

One response to “JESUS AND RAMADAN”
  1. Abraham Avatar
    Abraham

    GA WANI DAN LABARI MAI ……..
    ************************
    Wani saurayi ne musulmi yake
    soyayya da wata budurwa krista,
    soyayyarsu tayi karfi sosai kowa daga
    chikinsu yana tunanin bazai iya
    rayuwa ba ba tareda dayanba.
    Sai dai kash! Iyayen yarinyar sun
    tsaya kai da kafa chewa bazasu aura
    mata musulmi ba, haka shima
    saurayin iyayensa suka ki yadda ya
    auri krista.
    Amma duk da haka basu hakura da
    juna ba kuma kowanne daga chikinsu
    yaki auran wani daban.
    Sai saurayin wani lokachi ya kwanta
    jinya har aka kwantar da shi a asibiti
    amma wannan budurwar tashi krista
    saboda soyayya tana ta yi masa
    dawainiya da kai kawo.
    Watarana saurayin jinya tayi tsanani
    har yana kokarin chikawa lokachin
    kuma budurwar bata nan sai wani
    abokinsa.
    Sai abokinnasa da yaga mutuwa zaiyi
    saurayin sai yake kokarin bashi
    kalmar shahada la’alla ko za’a dache
    ya fada saboda yayi kyakkyawan
    karshe na chikawa da kalmar
    shahada.
    Amma inaaa! Saurayin yaki karba
    daga karshe ma chewa yayi shi fita
    zaiyi daga musulunchi ya koma
    kristaniti saboda ya samu daman
    haduwa da budurwarsa a lahira. Wai
    idan ya mutu yana musulmi
    budurwarsa kuma krista, bazasu
    hadu ba a lahira. Yana fadan wannan
    maganar sai ya chika.
    Chaaan kafin a fita dashi daga asibiti
    sai budurwar ta dawo tana tambayan
    abokin saurayinnata chewa ina yake
    saurayin. Sai abokin yache mata ai
    ya rasu. Amma bai fada mata abunda
    ya faru ba kafin rasuwannashi.
    Budurwar tayi ta kuka a asibiti dakyar
    aka bata haquri ta daina.
    Ita kuma daga karshe tache to
    wallahi zata musulunta. Sai aka
    Akache mata ai ba yanzu ya kamata
    ki musulunta ba. Tun da ya kamata ki
    musulunta saboda saurayinki ya
    samu damar aurenki, amma yanzu da
    ya mutu ai ko kin musulunta sai dai
    dan kanki.
    Sai tache ai ita bazata iya auran wani
    ba tunda saurayinta ya mutu, saboda
    haka zata musulunta tunda
    saurayinta musulmine inyaso su
    hadu a lahira, sai budurwa ta shiga
    addinin musulunchi.
    Kuma haka ta zauna tsawon
    rayuwarta bata auri kowaba har itama
    Allah yayi mata chikawa.
    *************
    FADAKARWA!
    Samari da ‘yan mata masu soyayyar
    wuche gona da iri sai a maida
    hankali a dinga yi saboda Allah.
    * Sau diyawa zakaji saurayi musulmi
    ya koma krista kuma daga zaran ka
    binchiki dalili sai kaga saboda wata
    krista che da yake so.
    * Wasu kuma a chikin musulunchin
    ake basu sharadin sai in sun shiga
    Shi’a za’a aura musu ko zasu daman
    auran yarinyarda suke so.
    ***
    Allah yasa mu dache.
    Allah ya bamu ikon aikata komai
    domin Shi.

Leave a Reply

Latest updates
Categories