Falalar Karanta Ayatul Kursiyyu Bayyan Sallan Farillah

image
ﻋﻦ ﺃﺑﻲ ﺃﻣﺎﻣﺔ
ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻪ، ﺃﻥ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ
ﻗﺎﻝ : ﻣﻦ ﻗﺮﺃ ﺁﻳﺔ ﺍﻟﻜﺮﺳﻲ ﺩﺑﺮ ﻛﻞ ﺻﻼﺓ ﻣﻜﺘﻮﺑﺔ،
ﻟﻢ ﻳﻤﻨﻌﻪ ﻣﻦ ﺩﺧﻮﻝ ﺍﻟﺠﻨﺔ ﺇﻻ ﺃﻥ ﻳﻤﻮﺕ.
Manzon Allah(Sallallahu alaihi wasallam) yace: ‘wanda ya karanta ayatul Kursiyyu bayan ko wata sallah ta farilla babu abinda zai hanashi shiga aljannah sai dai Mutuwa.
Hadisin ibn hibban da nasa’i sun rawaito. Sannan albani ya inganta shi.  Sannan ibn Qayyim yace hadisin an ruwaito shi daga hanyoyi dabam dabam wanda suke da’ifai. Amma in aka hadasu duka zasu nuna cewa hadisin yana da asali.
Allah ya bamu daman lazumtan wannnan aiki mai cike da Babban sakamako… Ameen.