ALKAKI DA RUWAN ZUMA(Dr. Mansur Sokoto)

Danna nan domin shiga Online Islamiyya.

Ana koyar da Hada baki, da Qur’ani da sauran su

ALKAKI DA RUWAN ZUMA
Ingantaccen Tarihin Fiyayyen Halitta
Sallallahu Alaihi Wa Ala Alihi
Wasallam
Fitowa ta 9
Me Ya Sa Aka Zabi Yankin
Larabawa?
3. Akwai yanayin kasar larabawan ita
kanta wadda ta fado a tsakiyar duniya
mai dauke da mutane a wancan lokaci.
Don haka yaduwar musulunci zuwa
sauran sassan duniya zai fi sauki a can
bisa ga ko ina daga sauran kasashe.
4. In ka hada wannan da kasancewar
daman can akwai dakin Allah na farko
a garin Makka, wanda kuma wadannan
bayin Allah suke girmama shi matuka
har ba sa bari ayi kowane irin fada ko
tashin hankali a kewayensa.
5. Ga kuma su larabawan suna rike da
sauran addinin annabi Ibrahim (AS)
duk da shigar da maguzanci da suka yi
a cikin sa. Misali, suna wankan janaba,
suna jana’iza, suna dawafi, suna azumi
a ranar Ashura. Idan kuma ka kalli
yanayinsu a auratayya da hukuncin
shika (saki) da idda da diyya dss zaka
san lalle suna da sauran abinda ya rage
ma su na addinin gaskiya. Daga cikin
abinda suke a kan sa na addinin annabi
Ibrahim (AS) akwai aikin Hajji da
Umra – ko da kuwa sun yi dawafi
tsirara a wasu lokuta. Ko da kuma
Quraishawa sun ki fita Arafat don ji-ji-
da-kai.
To, ka ga bayyanar musulunci a
wannan wurin a gyara kurakuransu ya
fi tasowar sa daga wani wuri inda za a
koya ma mutane sabon addinin da ba
su san makamarsa ba.
Mu kwana a nan. Gobe in Allah ya so
sai mu dora.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

One response to “ALKAKI DA RUWAN ZUMA(Dr. Mansur Sokoto)”
  1. Sulaiman Avatar

    Allah ya kara wa malam lfy.

Leave a Reply

Categories
Latest updates