Kada muyi kasa a gwiwa wurin yin rejistan N-Power

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Assalamu Alaikum.

Ƴan’uwa masu albarka sanin kowa ne cewa gobe 26 June 2020 Gwamnatin tarayya zata buɗe portal na fara ɗaukan sabbin ma’aikatan N-power, kuma abune sananne ƴan’uwanmu Musulmai suna da sakaci game da abubuwa irin wannn, shiyasa naso na jawo hankalin mu kan wannan lamari.

duk wanda yasan ya cika sharuɗan wannan aiki, kuma ya tabbata zaiyi aikin bawai kawai zai rinƙa karɓan kuɗi ne ba tare da aiki ba toh ya dace yayi rejista, domin hakan zata taimaka wa rayuwar sa harma zai iya taimaka wa wani.

Shafin da ake rejista: www.npower.gov.ng

Ranar fara rejista: 26 june 2020

Mu lura: wasu daga cikin ƴan’uwa Musulmai sukan shiga irin wannan tsari amma sai suƙi yin aikin da sukayi alƙawari zasuyi, kuma a ƙarshen wata a biyasu su ƙarɓa, toh masu wannan hali su sani cewa wannan ya tsaɓawa wa koyarwar Addinin Musulunci, kuma duk kuɗin da mutum ya karɓa ta wannan hanya haramun ne. Allah yasa mudace, ya kuma datar da wa’inda suke neman wannan aiki.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories