Danna nan domin shiga karatu Online
Malam yayi mana bayani akan yadda ake neman aure, tsarin da addini ya tanadar tare da tsare-tsare da ladubba kamar haka: 1.Siffofin Namijin da ya kamata a aura,i. Mai Addini.ii. Mai Ilimi.iii.Mai Sana’a.iv. Mai Asali.v. Mai Halaye Na Gari.vi. Lafiyayye.vii. Mai Tsafta.viii.Mai Haihuwa.x. Ki zama aji (Class) daya dashi.
·
A wannan darasin malam ya tattauna akan irin matar da mutum ya kamata ya aura, bisa doran Alkur’ani da Hadisi. 1.An umarci mutum ya auri mace saboda dalilai kamar hakai.Saboda Kyawun ta.ii. Saboda Martabarta.iii.Saboda dukiyarta.iv.Saboda Addininta.Amma sai Annabi (S.A.W) yace na umarceka da ka zabi mai addini.
·
Hukuncin Aure a Musulunci 1 Menene Hukuncin aure2 Rabe-Raben aure a musulunci Mutanen da dole ne su yi aure Mutanen da ya halatta su yi aure Mutanen da haramun ne suyi aure.
·
Darasi na Biyu a wannan shiri namu na Auratayya a wannan Tasha tamu mai albarka. Malam zaiyi mana nasiha akan Hikimar yin aure: Duk wanda yayi aure yabi Allah (S.W.T). Ka saka a ranka don Allah (S.W.T) da kuma koyi da Sunnar Annabi (S.A.W) za kayi aure. Aure yana kawar da sha’awa kuma yana runtse…
·