002 Auratayya: Hikimar Aure – Sheikh Aminu Ibrahim daurawa

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Darasi na Biyu a wannan shiri namu na Auratayya a wannan Tasha tamu mai albarka. Malam zaiyi mana nasiha akan Hikimar yin aure:

  1. Duk wanda yayi aure yabi Allah (S.W.T).
  2. Ka saka a ranka don Allah (S.W.T) da kuma koyi da Sunnar Annabi (S.A.W) za kayi aure.
  3. Aure yana kawar da sha’awa kuma yana runtse ido
  4. Aure yana tsare mutumdaga fadawa al fasha.
  5. Aure yana rage yaduwar alfasha, ‘ya’ya marasa uba yana kuma rage yaduwar cututtuka a cikin al’umma.
  6. Aure yana kara yawaitar al’umma na gari.
  7. Samun lada sanadiyyar mu’amalar aure da matarka.
  8. Duk wanda yayi aure to ya so kuma ya dabbaka abinda Annabi (S.A.W) ya ke so.
  9. Samun da ko ‘ya wanda za suke maka addu’a ko bayan ka mutu.
  10. Wanda ya haifi yaro ya mutu yana karami to yaron zai ceci iyayensa ranar Alkiyama.
  11. Samun ziriyyar da za ta tallafawa addinin Musulunci.
  12. Samun nutsuwa, kwanciyar hankali da kuma makoma ingantacciya.

Download
Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories