Fatawoyin Rahama By Dr. Sani Umar Rijiyar Lemo 28th May 2023

  1. Ya hallata Manomi ya nemi bashin kuɗi a wajen wani wanda ba manomi ba akan zai biya shi da wani abu da ya noma!
  2. Shin ana fitarwa Barkono zakka?
  3. Wani lokaci ne yankan aƙiƙa ya ke saraya ga wanda bai da hali yin aƙiƙa a yini na bakwai na haihuwa?
  4. Gaskiya ne Annabi Îsa (as) bai manyanta ba Allah ‎ ﷻ ya ɗauke shi zuwa gare Shi; amma Annabi Rahama ﷺ sai da ya kai shekara 40 aka aiko shi?
  5. Ya tabbata addu’a tana sauya ƙaddara?
  6. Ya tabbata in mutum yana sauraron waƙoƙi sai an wanke kunnuwansa kafin ya shiga Aljanna?
  7. Ya hallata yawaita yin addua ga ‘yanuwan mutum da suka rasu har ya zama kaman zikiri?
  8. Shawara ga wanda baya jin daɗin zama da matarsa da ba ta masa biyyaya saboda mahaifiyar sa ta ce ya haƙura ya zauna da ita a haka?
  9. Da gaske ne hadiśi ya zo da cewa ba a keɓance ranar Juma’a da azumin nafila?
  10. Shin ana ramawa wanda ya mutu da azumin Ramadana?
  11. Ya hallata mutum da yake kulawa da dukiyar mahaifinsa ya taɓa wani abu ba tare da ya nemi izinin mahaifinsa ba?
  12. Ya hallata mai kiwon kaji ta kashe magen da yake cin ‘ya’yan kajin da take kiwo?
  13. Matan da ba sa azumi da sallah sai an aurar da su saboda rashin karatu – shin yaya za su iya rama ibadun da suka yi sakacin aiwatarwa?
  14. Akwai banbancin lada tsakanin wanda ya yi Sallah da babbar riga da wanda yayi da jamfa kadai?
  15. Hukuncin wanda ya manta wanke ƙafa a wankan Janaba!
  16. Menene hukuncin wanda ya fara karanta aya sai ya ƙarasa da wata aya saboda mantuwa!
  17. Menene hukuncin ƙara karanta Suratul Ikhlas a raka’ar ƙarshe ta sallar Asuba?
  18. Hukuncin wanda ya bi Liman sallah alhali an ta da sallar minti ɗaya kafin shigar lokaci!
  19. Ya hallata wanda aka ba shi sautu ya riƙe duk wani sauki da aka samu na abin da yaje siya?
  20. Mace za ta iya yiwa wanda ba Muharramin ta ba Sallama?
  21. Wanda yake tsakiyar karatun Al-ƙur’ani sai aka yi masa sallama ko aka fara kiran sallah ko aka ambaci suna Annabi ﷺ – yaya zai yi?
  22. In Mamu ya riga Liman karanta tahiya zai iya sauke ɗan yatsan sa!
  23. Mutum zai iya yin Azumin Arafah ko da ana bin sa Ramuwar azumin Ramadan?

Fatawoyin Rahama By Dr. Sani Umar Rijiyar Lemo 27th May 2023

Shimfiɗa: Hikimar Hukunta Masu Laifuka a tsarin Sharia

Tambayoyi da Amsoshi da ke ciki:

  1. Hukuncin buɗe ‘event centres!
  2. Hukuncin gidaje da gonaku da ba a raba su gado ba saboda magadan ba sa faɗa!
  3. Wasu daga cikin haƙƙoƙin Annabi ﷺ akan al’umarsa.
  4. Hukuncin yin aikin Hajji ga ɗalibin da yake zama a Saudiya ba tare da samun takardar izini ba.
  5. Ya hallata mutum ya rinƙa nafiloli alhali ya yi tafi zuwa aikin Hajji.
  6. Da yin Waƙafi da maimaita zuwa Hajji wanne ya fi?
  7. Hukuncin wanda aka sace masa waya da bashin naira dubu ɗaya a layin da aka sace!
  8. Hukuncin fitar mai takaba!

Fatawoyin Rahama By Dr. Sani Umar Rijiyar Lemo 21st May 2023

Tambayoyi da Amsoshin da ke ciki –

  1. Shin ya inganta wani Sahabi ya taɓa hana Abu Huraira yawan zantar da hadisan Annabi ﷺ ?
  2. Wanda ya je wajen Mai Duba alhali yana zaton Malami ne – yaya zai yi ya tuba?
  3. Idan mutum ya hau a dai-daita sahu bai samu ya biya mai a dai-daita sahun ba- yaya zai yi da kuɗin?
  4. Banbancin tsakanin Taƙwa da Imani
  5. Wanda zai yi sallar nafila zai iya maimaita sura ko aya ɗaya?
  6. Ya hallata a keɓence sallar asuba a rinƙa karanta mata Suratul Mulk!
  7. Ana iya karanta ‘amin’ bayan Liman ya karanta ayar AmanarRasulu– a Salla?
  8. Mutum zai iya barin gidan mahaifinsa zuwa wani waje saboda ƙiyyaya da ake nuna masa!
  9. Ya hallata mutum ya sayi kaya da Kwastam suke karɓa a wajen mutane su yi gwanjonsu!
  10. Mutumin da yake ɗaukar kayan mahaifinsa yana amfani da su- zai dawo da su a matsayin kayan gado in mahaifin ya rasu?
  11. Hukuncin wanda zai yi sadaƙa amma baya so a san shi, sai ya fadi sunan wani a matsayin shi ne ya bada sadaƙar!
  12. Mai Sallah zai iya yin taku don kashe wayarsa da take ƙara!
  13. Hukuncin wacce jinin al’adarta yake zuwa yana ɗaukewa
  14. Yaya hukuncin jinin wanke mahaifa!
  15. Jinin da ya biyo bayan ɓari jinin biki ne?
  16. Ya hallata mace ta zubar da ciki in mijin da ta aura – ya saketa – yana da mata hudu?
  17. Wanda ya zo Sallar Îdi ya samu Liman yana zaman tahiya – ya samu Sallar Îdi
  18. Hukuncin yin ɗawafi dauke da ruwan zam-zam!
  19. Mai aikin Hajji zai iya azumin nafila!
  20. Ya inganta azumin Sitta Shawwaal ana iya yinsa a wasu wattani?
  21. Hukuncin wanda ya ci abinci a Ramadan bayan fitowar alfijir!

Fatawoyin Rahama By Dr. Sani Umar Rijiyar Lemo 20th May 2023

Shimfida: Samun Masu Ƙoƙarin Gyra a cikin Al’uma Kariya ce Ga Wannan Al’umar

Tambayoyi da Amsoshi da ke ciki:

  1. Hukuncin sa Wata da Tauraro a husumiyar Massallaci!
  2. Hukuncin tsintuwar ƙananan dabbobi!
  3. Laifi ne miji ya ɗinka wa matarsa kaya mai tsada fiye da wanda ya ɗinkawa mahaifiyarsa?
  4. Wani lokaci ne ya wajaba a daina kwana da yara?
  5. Hukuncin wanda ya zubar da ciki sannan ya yi nadama daga baya!
  6. Hukuncin abokin karatu ya sa wa abokinsa Hannu da bai zo makaranta ba!
  7. Sallar Matafiyi da ya dawo gida bai sami damar yin sallar ƙasaru lokacin da yake halin tafiya!
  8. Ɗan siyasa mai wakiltar musulmi da kirista – idan ya ya ginawa musulmai massallaci – zai iya ginawa Kiristoci coci?
  9. In mutum ya ɗauko yaro daga gidan marayu, za a kira shi da sunan mahaifinsa ko sunan wanda yake kulawa da shi?
  10. Shin ƙafar mace al’aura ce? Yaya matsayin bayyanar ƙafar mace a Sallah?
  11. Yaya gadon mata- Maza zai kasance?
  12. su waye‘ Rumawa’ da ‘Farisawa’ da Annabi ﷺ ya yaƙa!
  13. Ya hallata mutum karɓi kuɗin ma’aikaci da ya ke ƙarƙashin sa ya rubuta cewa ya zo aiki alhali bai zo ba?
  14. Hukuncin wanda ake kawo masa sukar abokansa amma ba ya gaya ma abokansa da ake sukar su!
  15. Hukuncin sallar wanda ya manta da wata sunnar salla!
  16. Menene hukuncin haɗa kuɗin magada a account ɗaya- kuma za a cire musu zakka?