Aljannah gidan hutu

·

·

Domin neman ƙarin bayani danna nan

Mai rubutu: Hamza Diso


Allah madaukakin sarki ya tanadi Aljanna don muminai masoya Allah akan aikin da sukayi a duniya na imani da jajircewa akan tafarkin Annabta.

Aljanna hawa-hawa ce, takai hawa Dari(100) tsakanin ko wanne hawa da na saman sa akwai tafiyar shekara dari, wadanda suke kasa suna hango na Sama kamar yadda muke ganin taurari anan duniya.

Aljanna ta hada dukkannin wani nau’i najin dadi da hutu Wanda ka sani da wanda baka sani ba, acikinta akwai abinda babu Wanda ya taba ganin irin sa a duniya, babu Wanda ya tabajin labarinsa, babu Wanda ya taba raya shi a zuciya.

Ginin Aljannah kala-kala ne, akwai Aljannar Azurfa wadda komai Na cikinta Azurfa ce, akwai kuma ta zinare, akwai manyan gine-gine masu ban ‘Kaye, akwai kuma babban tanti Na lu’ulu’u rarakakke, tsahonsa a Sama yakai mil 70( kimanin 130 km) sannan yana da fadin gaske, a kowanne gefe daga cikinsa akwai kuyanga, kuma kuyangin basa ganin juna saboda girman gurin.

Akwai koramu kala-kala, da abubuwan sha iri-iri masu ‘dan’dano daban daban, akwai wata giya da ake hadata da wani abunsha mai suna Kafur, shi kafur din idaniya ce datake bubbugowa a gidajen manyan yan Aljanna, su suna iya shan kafur din zallah, akwai dukkanin nau’ikan ‘ya’yan itace Na alfarma wadanda ‘dan’danon su ya sabawa duk abinda ka sani a duniya, ga bishiyu masu inuwar gaske masu dauke da Kayan marmari, saboda nauyin Kayan marmarin zakaga reshe ya kwanto kasa sosai.

Ga Yara masu hidima a ko ina cikin Gidan suna dauke da akusai, cikin akusan akwai nau’ikan abubuwan ci daban-daban, idan ka kalli yaran sai ka zaci lu’ulu’u ne aka wawwatsa a ko’ina cikin Gidan saboda kyawunsu.

Babu rana babu sanyi, babu dare babu yini, ba wahala ba gajiya ba bakin ciki ko damuwa, sai tsantsar mulki da ni’ima masu girman gaske.

Ga ganin Allah madaukaki mai rinjaye gagara misali, da kuma yin magana da Allah, ga Annabi (salatin Allah da amincinsa a gareshi) wani dadi ne ya wuce wannan??!!

Ba fitsari ba bayan Gida ba kaki, mafi talaucin yan Aljanna shine yake da kimanin ninkin duniya sau goma.

Allah bamuyi tanadin komai ba, amma mu musulmi ne,ka Sanya mu cikin Ni’imarka ka gafarta mana, kasanya mu cikin wadanda zasu gaji Aljanna

Gadon Aljanna shine a baka taka sannan a kara maka data yan wuta, don kowa yana da guri a Aljanna, to kafirai tunda suna wuta sai a rabawa muminai gidajensu

Allah rahamarka muke kwadayi, mu masu laifi ne

Leave a Reply

Latest updates
Categories