BAYANI A KAN BUKIN MAULIDI KASHI NA DAYA: (1)(Dr Ibrahim Jalo Jalingo)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Yau alhamis 5/3/1434 H 17/1/2013
M tsakaninmu da ranar goma sha
biyu ga watan Rabii’ul Awwal
kwana 7 ne kacal, sannan kamar
yadda aka sani ne cewa wannan
rana ta 12/3/ ita ce ranar da wasu
daga cikin masu ikirarin Musulunci
ke bukin ranar haifuwar Annabi
Muhammad mai tsira da amincin
Allah, saboda neman lada da falala
a wurin Allah, duk kuwa da cewa
rikon wannan rana a matsayin Idi
bidi’a ne wurin dukkan Maluman
Musulunci! Allah Sarki! Haka dai
Haidan yake badda mutane cikin
mamaki wani lokaci! Allah
Madaukakin Sarki yana cewa cikin
Suratu Faatir aya ta 8:-
((ﺃﻓﻤﻦ ﺯﻳﻦ ﻟﻪ ﺳﻮﺀ ﻋﻤﻠﻪ ﻓﺮﺍﻩ ﺣﺴﻨﺎ ﻓﺎﻥ ﺍﻟﻠﻪ
ﻳﻀﻞ ﻣﻦ ﻳﺸﺎﺀ ﻭﻳﻬﺪﻱ ﻣﻦ ﻳﺸﺎﺀ ﻓﻼ ﺗﺬﻫﺐ ﻧﻔﺴﻚ
ﻋﻠﻴﻬﻢ ﺣﺴﺮﺍﺕ ﺍﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻢ ﺑﻤﺎ ﻳﺼﻨﻌﻮﻥ )).
Ma’ana: ((yanzu wanda aka
kawata masa mummunan aikinsa
har ya gan shi wani abu Mai kyau
“yana daidai da waninsa?” saboda
haka lalle Allah yana batar da
wanda yake so, kuma ya shiryar da
wanda yake so, kada ranka ya
halaka a kansu saboda bakin ciki.
Lalle Allah Masani ne ga abin da
suke sana’antawa)). Intaha.
Ni a nan, a bisa dogara da ayah ta
104 a cikin Suratu Aali inda Allah
Madaukakin Sarki Ya ce:-
(( ﻭﻟﺘﻜﻦ ﻣﻨﻜﻢ ﺃﻣﺔ ﻳﺪﻋﻮﻥ ﺍﻟﻰ ﺍﻟﺨﻴﺮ ﻭﻳﺄﻣﺮﻭﻥ
ﺑﺎﻟﻤﻌﺮﻭﻑ ﻭﻳﻨﻬﻮﻥ ﻋﻦ ﺍﻟﻤﻨﻜﺮ ﻭﺃﻭﻟﺌﻚ ﻫﻢ
ﺍﻟﻤﻔﻠﺤﻮﻥ )).
Ma’ana: ((A samu wata al’umma
daga cikinku da za ta yi kira zuwa
ga alheri, sannan ta umurni da
abin da Shari’ah ta sani, kuma ta yi
hani ga abin da Shari’ah bata sani
ba. To su wadannan Al’umma sune
masu rabauta)). Intaha. Da kuma
dogara kan aya ta 78, da 79 cikin
Suratul Maa’idah inda Allah
Madaukaki ya yi maga a kan
Banuu Isaraa’iil ya ce:-
(( ﻟﻌﻦ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﻛﻔﺮﻭﺍ ﻣﻦ ﺑﻨﻲ ﺍﺳﺮﺍﺋﻴﻞ ﻋﻠﻰ ﻟﺴﺎﻥ
ﺩﺍﻭﺩ ﻭﻋﻴﺴﻰ ﺍﺑﻦ ﻣﺮﻳﻢ ﺫﻟﻚ ﺑﻤﺎ ﻋﺼﻮﺍ ﻭﻛﺎﻧﻮﺍ
ﻳﻌﺘﺪﻭﻥ. ﻛﺎﻧﻮﺍ ﻻ ﻳﺘﻨﺎﻫﻮﻥ ﻋﻦ ﻣﻨﻜﺮ ﻓﻌﻠﻮﻩ ﻟﺒﺌﺲ
ﻣﺎ ﻛﺎﻧﻮﺍ ﻳﻔﻌﻠﻮﻥ )).
Ma’ana: ((An la’anci wadanda suka
kafirta daga Banu Isaa’iil a bisa
harshen Daawuuda da Isa Dan
Maryam, saboda irin yadda suka yi
sabo, suka kasance suna ketare
iyaka. Suka kasance ba sa hana
juna yin mummunan aikin da suke
aikatawa. Wallahi abin da suka
kasance suna aikatawa ya yi muni)
). Intaha. Da kuma dogara kan
hadithin da Imam Muslim ya
ruwaito hadithi na 49 inda Annabi
mai tsira da amincin Allah yake
cewa:-
(( ﻣﻦ ﺭﺃﻯ ﻣﻨﻜﻢ ﻣﻨﻜﺮﺍ ﻓﻠﻴﻐﻴﺮﻩ ﺑﻴﺪﻩ ﻓﺎﻥ ﻟﻢ ﻳﺴﺘﻄﻊ
ﻓﺒﻠﺴﺎﻧﻪ ﻓﺎﻥ ﻟﻢ ﻳﺴﺘﻄﻊ ﻓﺒﻘﻠﺒﻪ ﻭﺫﻟﻚ ﺍﺿﻌﻒ
ﺍﻻﻳﻤﺎﻥ )).
Ma’ana: ((Wanda duk ya ga
munkari daga cikinku sai ya jirkita
shi da hannunsa, in kuma ba zai
iya ba, sai ya jirkita shi da
harshensa, in kuma ba zai iya ba
sai ya jirkita shi da zuciyarsa,
wannan shi ne mafi raunin Imani)).
Intaha. Da kuma dogara kan
maganar Sahabin Annabi
Abdullahi Dan Mas’ud Allah ya
kara masa yarda, wacce ta zo cikin
littafin Ibnu Wadh,dhah shafi na 11
da littafin Ali’itisaam na Imamush
Shaatibii 1/107 inda ya ce:-
(( ﺍﺗﺒﻌﻮﺍ ﻭﻻ ﺗﺒﺘﺪﻋﻮﺍ ﻓﻘﺪ ﻛﻔﻴﺘﻢ)).
Ma’ana: ((Ku bi -abin da Annabi ya
zo da shi- kada ku kirkiri bidi’ah,
domin an gama muku kome -na
addini-)). Dankuma dogara har
yanzu a kan maganar shi Sahabi
Abdullahi Dan Mas’uud wacce ta
zo cikin littafin Ibnu Wadh’dhah
shafi na 11 da kuma Sunanud
Daarami 1/68-69 a inda ya ce
lokacin da ya wuce wani mai
wa’azi a cikin masallaci yana ce wa
mutane: ku yi Subhanallah kafa
goma, ku yi la’laha illalah kafa
goma, sai ya ce da su:-
(( ﻭﻳﺤﻜﻢ ﻳﺎ ﺃﻣﺔ ﻣﺤﻤﺪ ﻣﺎ ﺍﺳﺮﻉ ﻫﻠﻜﺘﻜﻢ ! ﻫﺆﻻﺀ
ﺻﺤﺎﺑﺔ ﻧﺒﻴﻜﻢ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻣﺘﻮﺍﻓﺮﻭﻥ
ﻭﻫﺬﻩ ﺛﻴﺎﺑﻪ ﻟﻢ ﺗﺒﻞ ﻭﺃﺗﻴﺘﻪ ﻟﻢ ﺗﻜﺴﺮ ﻭﺍﻟﺬﻱ ﻧﻔﺴﻲ ﺑﻴﺪﻩ
ﺍﻧﻜﻢ ﻟﻌﻠﻰ ﻣﻠﺔ ﻫﻲ ﺃﻫﺪﻯ ﻣﻦ ﻣﻠﺔ ﻣﺤﻤﺪ ﺍﻭ ﻣﻔﺘﺘﺤﻮﺍ
ﺑﺎﺏ ﺿﻼﻟﺔ. ﻗﺎﻟﻮﺍ ﻳﺎ ﺃﺑﺎ ﻋﺒﺪ ﺍﻟﺮﺣﻤﻦ ﻣﺎ ﺍﺭﺩﻧﺎ ﺍﻻ
ﺍﻟﺨﻴﺮ ﻗﺎﻝ ﻭﻛﻢ ﻣﺮﻳﺪ ﻟﻠﺨﻴﺮ ﻟﻦ ﻳﺼﻴﺒﻪ ﺍﻥ ﺭﺳﻮﻝ
ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺣﺪﺛﻨﺎ ﺍﻥ ﻗﻮﻣﺎ ﻳﻘﺮﺀﻭﻥ
ﺍﻟﻘﺮﺍﻥ ﻻ ﻳﺠﺎﻭﺯ ﺗﺮﺍﻗﻴﻬﻢ ﻭﺍﻳﻢ ﺍﻟﻠﻪ ﻣﺎ ﺍﺩﺭﻱ ﻟﻌﻞ
ﺍﻛﺜﺮﻫﻢ ﻣﻨﻜﻢ ﺛﻢ ﻭﻟﻰ ﻋﻨﻬﻢ )).
Ma’ana: ((kaitonku ya ku al’ummar
Muhammad mamakin saurin
halakarku! Wadannan Sahabban
annabinku ne mai tsira da amincin
Allah ga su nan da yawa,
wadannan tufafinsa ne ba su gama
yagewa ba, wadannan butocinsa
ne ba su gama fashewa ba. Ina
rantsuwa da Wanda raina yake
hannunsa lalle ne ku ko dai kuna
kan wani addini ne da ya fi addinin
Muhammad shiriya ko kuwa ku
masu bude kofar bata ne. Sai suka
ce wallahi baban Abdurrahman
babu abin da muke nufi sai alheri.
Sai ya ce ai da yawa mai son alheri
ba zai taba samun sa ba. Lalle
Manzon Allah mai tsira da amincin
Allah ya gaya mana cewa akwai
wasu mutane da za su rika karanta
Alkur’ani amma kuma ba zai wuce
makogoronsu ba, Ina rantsuwa da
Allah watakila mafi yawansu daga
cikinku suke. Daga nan sai ya juya
ya bar su)). Intaha. Da kuma
dogara kan maganar babban
Taabi’ii Hasanul Basarii wacce ta
zo cikin littafin Ibnu Wadh’dhah, da
littafin Alitisam na Shaatibii 1/111
inda ya ce: ((Mai yin bidi’ah ba zai
Kara kokari cikin azuminsa na
bidi’ah ba, ko sallarsa ta bidi’ah ba,
face hakan ya nisantar da shi daga
Allah)). Intaha.
Dogara kan wadannan ayoyi da
hadithai da maganganun Sahabbai
da Taabi’ai da kuka ji su yanzu ne
ya sa muke gargadin Al’ummar
Musulmi, muke hana su rikon ranar
haihuwar Manzon Allah Mai tsira
da amincin Allah a matsayin ranar
Idi, muke musu gargadin rikon
bukin maulidi a matsayin wani abu
na addini da ake neman lada da
shi a wurin Allah Madaukakin
Sarki!
Saboda abu ne tabbatacce wurin
Maluman Musulunci cewa Annabi
Mai tsira da amincin Allah bai yi
bukin maulidi ba, Sahabbai ba su
yi bukin maulidi ba, Taabi’ai ba su
yi bukin maulidi ba, Taabi’ut
Taabi’in ba su yi bukin maulidi ba.
Duk kuwa abin da ba zama addini
ba a zamanin Sahabbai, da
Taabi’ai, da Taabi’ut Taabi’in tare
da kasancewar sababin yin sa a
lokacin nasu’ da kuma ikon yin sa
daga gare su yana nan’ amma
kuma babu Wanda ya yi shi daga
cikinsu, to lalle wannan abin babu
ta yadda za a yi ya zamanto addini
karbabbe a wurin na bayansu har
zuwa tashin Kiyama.
Yan’uwa Musulmi! Lalle shi rikon
ranar maulidi a matsayin Idi, da
maida shi ranar buki, ba a fara yin
shi ba cikin wannan Al’umma sai
cikin karni na hudu na hijirar
Annabi Mai tsira da amincin Allah’
watau sai a cikin shekara ta dari
uku da settin da biyu (362).
Sannan mutumin da ya fara yin
wannan buki na maulidi shi ne
wani sarki dan Shi’ah Fadimiyyah
Mai suna Almu’izzu li Dininl Lah a
garin Alkahira’ kamar yadda yake
rubuce cikin littattafan Musulunci
da tarihi, da wasunsu, kuna iya
duba wadannan littattafan:-
ﺍﻟﻤﻮﺍﻋﻆ ﻭﺍﻻﻋﺘﺒﺎﺭ ﺑﺬﻛﺮ ﺍﻟﺨﻄﻂ ﻭﺍﻻﺛﺎﺭ
ﻟﻠﻤﻘﺮﻳﺰﻱ ١/ ٤٩٠، ﻭﺻﺒﺢ ﺍﻷﻋﺸﻰ ﻓﻲ ﺻﻨﺎﻋﺔ
ﺍﻹﻧﺸﺎﺀ ﻟﻠﻘﻠﻘﺸﻨﺪﻱ ٣/ ٤٩٨، ﻭﺗﺎﺭﻳﺦ ﺍﻻﺣﺘﻔﺎﻝ
ﺑﺎﻟﻤﻮﻟﺪ ﺍﻟﻨﺒﻮﻱ ﻟﻠﺴﻨﺪﻭﺑﻲ ﺹ٦٩، ﻭﺃﺣﺴﻦ ﺍﻟﻜﻼﻡ
ﻓﻴﻤﺎ ﻳﺘﻌﻠﻖ ﺑﺎﻟﺴﻨﺔ ﻭﺍﻟﺒﺪﻋﺔ ﻣﻦ ﺍﻷﺣﻜﺎﻡ ﻟﻤﺤﻤﺪ
ﺑﺨﻴﺖ ﺹ٤٤، ٤٥، ﻭﺍﻟﻤﺤﺎﺿﺮﺍﺕ ﺍﻟﻔﻜﺮﻳﺔ ﻟﻠﺸﻴﺦ
ﻋﻠﻲ ﻓﻜﺮﻱ ﺹ٨٤، ﻭﺍﻹﺑﺪﺍﻉ ﻓﻲ ﻣﻀﺎﺭ ﺍﻻﺑﺘﺪﺍﻉ
ﻟﻠﺸﻴﺦ ﻋﻠﻲ ﻣﺤﻔﻮﻅ ﺹ١٢٦، ﻭﺍﻟﺘﺎﺭﻳﺦ ﺍﻟﻌﺒﺎﺳﻲ
ﻭﺍﻟﻔﺎﻃﻤﻲ ﻟﻠﺸﻴﺦ ﺍﺣﻤﺪ ﻣﺨﺘﺎﺭ ﺍﻟﻌﺒﺎﺩﻱ ﺹ٢٦١،
٢٦٢ .
Almawaa’izu wa Litibaar na
Maqriizii 1/490, da Subhul A’ashaa
na Qalqashandii 3/498, da
Taariikhu Lihtifaali Bil Maulidin
Nabawii na Sanduubii shafi na 69,
da Ahsanul Kalam fi ma yataallaqu
bis Sunnati wal Bidi’ati minal
Ahkam na Muhammad Bakhiit
shafi na 44,45, da
Almuhadharaatul Fikriyyah na Ali
Fikrii shafi na 84, da Al’ibdaa fi
Madharri Libtidaa na Ali Mahfuuz
shafi na 126, da Taarikhul Abbaasii
wal Faatimii na Ahmad Mukhtaar
Al’abbadii shafi na 261,262.
MALUMAN MUSULUNCI DABAN
DABAN SUN HANA YIN BUKIN
MAULIDI:
Yan’uwa Musulmi! Lalle da yawa
daga cikin maluman Musulunci sun
gargadi Al’umma sun hana su yin
bukin maulidi da rikon shi a
matsayin wata ibadah da za a nemi
lada wurin Allah da ita, kuma sun
bayyanar da cewa yin bukin
maulidi bidi’a ce kuma bata.
Daga cikin wadannan malamai
akwai manya manyan malumanmu
na mazhabar Malikiyyah, kamar
Ibnul Hajj wanda ya rasu a
shekarar hijira ta 732 watau yau da
rasuwarsa shekaru 702 ke nan da
suka wuce, da kuma Umarul
Faakihaanii wanda ya rasu a
shekarar hijira ta 734 watau yau da
mutuwarsa shekara 700 ke nan da
suka wuce, da kuma Ibraahimush
Shaatibii wanda ya rasu a shekarar
hijira ta 690 watau yau da
rasuwarsa shekara 744 ke nan da
suka wuce, da kuma uwa-uba
Sheik Uthmanu Dan Fodiyo wanda
ya rasu a shekarar hijira ta 1234
watau yau shekara 201 ke nan da
rasuwarsa.
Amma Sheik Ibnul Hajj ga abin da
yake cewa cikin littafin Almudkhal
2/2, da 2/10-11 :-
(( ﻭﻣﻦ ﺟﻤﻠﺔ ﻣﺎ ﺍﺣﺪﺛﻮﻩ ﻣﻦ ﺍﻟﺒﺪﻉ ﻣﻊ ﺍﻋﺘﻘﺎﺩﻫﻢ ﺍﻥ
ﺫﻟﻚ ﻣﻦ ﺍﻛﺒﺮ ﺍﻟﻌﺒﺎﺩﺍﺕ ﻭﺍﻇﻬﺮ ﺍﻟﺸﻌﺎﺋﺮ ﻣﺎ ﻳﻔﻌﻠﻮﻧﻪ
ﻓﻲ ﺷﻬﺮ ﺭﺑﻴﻊ ﺍﻻﻭﻝ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﻮﻟﺪ ﻭﻗﺪ ﺍﺣﺘﻮﻯ ﻋﻠﻰ
ﺑﺪﻉ ﻭﻣﺤﺮﻣﺎﺕ ﺟﻤﻠﺔ ﻓﻤﻦ ﺫﻟﻚ ﺍﺳﺘﻌﻤﺎﻟﻬﻢ ﺍﻟﻤﻐﺎﻧﻲ
ﻭﻣﻌﻬﻢ ﺁﻻﺕ ﺍﻟﻄﺮﺏ(( ﺍﻟﻰ ﺍﻥ ﻗﺎﻝ)) : ﻭﺍﻥ ﺧﻼ ﻣﻨﻪ
ﻭﻋﻤﻞ ﻃﻌﺎﻣﺎ ﻓﻘﻂ ﻭﻧﻮﻯ ﺑﻪ ﺍﻟﻤﻮﻟﺪ ﻭﺩﻋﺎ ﺍﻟﻴﻪ
ﺍﻻﺧﻮﺍﻥ ﻭﺳﻠﻢ ﻣﻦ ﻛﻞ ﻣﺎ ﺗﻘﺪﻡ ﺫﻛﺮﻩ ﻓﻬﻮ ﺑﺪﻋﺔ
ﺑﻨﻔﺲ ﻧﻴﺘﻪ ﻓﻘﻂ ﺇﺫ ﺍﻥ ﺫﻟﻚ ﺯﻳﺎﺩﺓ ﻓﻲ ﺍﻟﺪﻳﻦ ﻭﻟﻴﺲ
ﻣﻦ ﻋﻤﻞ ﺍﻟﺴﻠﻒ ﺍﻟﻤﺎﺿﻴﻦ ﻭﺍﺗﺒﺎﻉ ﺍﻟﺴﻠﻒ ﺍﻭﻟﻰ ﺑﻞ
ﺃﻭﺟﺐ ﻣﻦ ﺍﻥ ﻳﺰﻳﺪ ﻧﻴﺔ ﻣﺨﺎﻟﻔﺔ ﻟﻤﺎ ﻛﺎﻧﻮﺍ ﻋﻠﻴﻪ
ﻷﻧﻬﻢ ﺍﺷﺪ ﺍﺗﺒﺎﻋﺎ ﻟﺴﻨﺔ ﺭﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ
ﻭﺳﻠﻢ ﻭﺗﻌﻈﻴﻤﺎ ﻟﻪ ﻭﺳﻨﺘﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ
ﻭﻟﻬﻢ ﻗﺪﻡ ﺍﻟﺴﺒﻖ ﻓﻲ ﺍﻟﻤﺒﺎﺩﺭﺓ ﺍﻟﻰ ﺫﻟﻚ ﻭﻟﻢ ﻳﻨﻘﻞ ﻋﻦ
ﺍﺣﺪ ﻣﻨﻬﻢ ﺍﻧﻪ ﻧﻮﻯ ﺍﻟﻤﻮﻟﺪ ﻭﻧﺤﻦ ﻟﻬﻢ ﺗﺒﻊ ﻓﻴﺴﻌﻨﺎ ﻣﺎ
ﻭﺳﻌﻬﻢ )).
Ma’ana: ((Yana daga cikin jumlar
abin da suka kirkira na bidi’o’i tare
da akidar cewa hakan yana daga
cikin manyan ibadodi, kuma yana
daga cikin alamomin Musulunci
mafi fita fili: abin nan da suke
aikatawa cikin watan Rabii’ul
Awwal na bukin maulidi. Shi dai
maulidi ya tattari abubuwan
haramun da yawa a dunkule, daga
cikinsu akwai wake-wake da suke
yi tare da Kayan kade-kade …. To
amma idan yin maulidi ya wifinta
daga yin wake-wake tare da kayan
kade-kade mai yin maulidin ya yi
abinci kawai ya yi nufin maulidi da
shi ya kira yan’uwa zuwa cin
abincin, to, yin hakan ya zama
bidi’ah saboda niyyar maulidin da
ya yi, domin niyyar maulidin kari ne
a cikin Addini ba ya kuma daga
cikin ayyukan Salaf Magabata ba,
bin Magabata kuwa shi ne ya fi
dacewa, kai shi ne ma wajibi da a
ce mutum zai kara wani abu
sabanin abin da suka kasance a
kansa, domin su Magabata su ne
suka fi kowa yin koyi da Manzon
Allah, kuma su ne suka fi kowa
girmama shi da girmama sunnarsa,
kuma su suke da kafar rigaya
wajen takawa zuwa ga abin da
yake alheri ne, babu kuma mutum
daya da ya ciro yin niyyar maulidi
daga dayansu, mu kuwa sauran
Musulmi mabiya ne gare su,
dukkan abin da ya wadatar da su
na addini shi ne zai wadatar da
mu)). Intaha.
Sannan Imamul Faakihaanii ya ce
cikin Risalarsa ta maulidi mai suna
Almurid fil Kalaami alaa Hukmil
Maulid :-
(( ﻻ ﺍﻋﻠﻢ ﻟﻬﺬﺍ ﺍﻟﻤﻮﻟﺪ ﺍﺻﻼ ﻓﻲ ﻛﺘﺎﺏ ﻭﻻ ﺳﻨﺔ ﻭﻻ
ﻳﻨﻘﻞ ﻋﻤﻠﻪ ﻋﻦ ﺍﺣﺪ ﻣﻦ ﻋﻠﻤﺎﺀ ﺍﻻﻣﺔ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﻫﻢ
ﺍﻟﻘﺪﻭﺓ ﻓﻲ ﺍﻟﺪﻳﻦ ﺍﻟﻤﺘﻤﺴﻜﻮﻥ ﺑﺂﺛﺎﺭ ﺍﻟﻤﺘﻘﺪﻣﻴﻦ ﺑﻞ
ﻫﻮ ﺑﺪﻋﺔ ﺍﺣﺪﺛﻬﺎ ﺍﻟﺒﻄﺎﻟﻮﻥ ﻭﺷﻬﻮﺓ ﻧﻔﺲ ﺍﻋﺘﻨﻰ ﺑﻬﺎ
ﺍﻻﻛﺎﻟﻮﻥ ﺑﺪﻟﻴﻞ ﺍﻧﺎ ﺍﺫﺍ ﺃﺩﺭﻧﺎ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻷﺣﻜﺎﻡ ﺍﻟﺨﻤﺴﺔ
ﻗﻠﻨﺎ ﺍﻣﺎ ﺍﻥ ﻳﻜﻮﻥ ﻭﺍﺟﺒﺎ ﺍﻭ ﻣﻨﺪﻭﺑﺎ ﺍﻭ ﻣﺒﺎﺣﺎ ﺍﻭ
ﻣﻜﺮﻭﻫﺎ ﺍﻭ ﻣﺤﺮﻣﺎ ﻭﻫﻮ ﻟﻴﺲ ﺑﻮﺍﺟﺐ ﺇﺟﻤﺎﻋﺎ ﻭﻻ
ﺑﻤﻨﺪﻭﺏ ﻻﻥ ﺣﻘﻴﻘﺔ ﺍﻟﻤﻨﺪﻭﺏ ﻣﺎ ﻃﻠﺒﻪ ﺍﻟﺸﺮﻉ ﻣﻦ
ﻏﻴﺮ ﺫﻡ ﻋﻠﻰ ﺗﺮﻛﻪ ﻭﻫﺬﺍ ﻟﻢ ﻳﺄﺫﻥ ﻓﻴﻪ ﺍﻟﺸﺮﻉ ﻭﻻ
ﻓﻌﻠﻪ ﺍﻟﺼﺤﺎﺑﺔ ﻭﻻ ﺍﻟﺘﺎﺑﻌﻮﻥ ﻭﻻ ﺍﻟﻌﻠﻤﺎﺀ ﺍﻟﻤﺘﺪﻳﻨﻮﻥ
ﻓﻴﻤﺎ ﻋﻠﻤﺖ ﻭﻫﺬﺍ ﺟﻮﺍﺑﻲ ﻋﻨﻪ ﺑﻴﻦ ﻳﺪﻱ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻥ ﻋﻨﻪ
ﺳﺌﻠﺖ ﻭﻻ ﺟﺎﺋﺰ ﺍﻥ ﻳﻜﻮﻥ ﻣﺒﺎﺣﺎ ﻻﻥ ﺍﻻﺑﺘﺪﺍﻉ ﻓﻲ
ﺍﻟﺪﻳﻦ ﻟﻴﺲ ﻣﺒﺎﺣﺎ ﺑﺈﺟﻤﺎﻉ ﺍﻟﻤﺴﻠﻤﻴﻦ ﻓﻠﻢ ﻳﺒﻖ ﺍﻻ ﺍﻥ
ﻳﻜﻮﻥ ﻣﻜﺮﻭﻫﺎ ﺍﻭ ﺣﺮﺍﻣﺎ.(( ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma’ana: ((Ban san wata hujja da
za ta halatta yin maulidi ba a cikin
Alkur’ani da Sunnah, kuma ba a
nakalto yin bukin maulidi koda
daga mutum daya ba cikin
maluman Al’umma wadanda su ne
abin koyi a cikin Addini , kuma su
ne ke riko da maganganun
magabata, kai, abin da dai yake
ciki shi ne: shi dai maulidi wata
biri’ah ce da marasa aikin yi suka
kirkira kuma sha’awar son rai ce da
masu cin dukiyar mutane cikin
karya suka runguma, saboda shi
dai bukin maulidi idan muka
shimfida shi a kan hukunce-
hukuncin nan guda biyar sai mu
ce: ko dai ya zama wajibi, ko kuwa
ya zama mustahabbi, ko kuwa ya
zama mubaahi, ko kuwa ya zama
makruuhi, ko kuwa ya zama
haraamun, to in mun yi hakan za
mu ga cewa shi dai ba wajibi ba ne
bisa Ijmaa’in Malamai, shi kuwa ba
mustahabbi ba ne domin abin da
ake nufi da mustahabbi shi ne abin
da Shari’ah ta ce a yi ba tare da an
zargi Wanda ya ki yi ba, shi kuwa
maulidi Shari’ah ba ta ce a yi shi
ba, kuma ni a sanina Sahabbai, da
Taabi’ai, da malamai masu riko da
Addini ba su yi shi ba, wannan shi
ne jawabina a gaban Allah a kan
bukin maulidi in har aka tambaye
ni. Kuma ba zai halatta ba a ce
Maulidi ya zama mubaahi saboda
kirkiran wani abu cikin addini ba
zai zama mubaahi ba a bisa
Ijmaa’in Musulmi, saboda haka
babu abin da ya rage face maulidi
ya zama makruuhi ko kuwa
haramun)). Intaha.
Sannan Imamush Shaatibii ya ce –
a lokacin da yake yin bayanin
ma’anar bidi’ah- cikin littafinsa mai
suna Alitisam 1/50,53 :-
(( ﻋﺒﺎﺭﺓ ﻋﻦ ﻃﺮﻳﻘﺔ ﻓﻲ ﺍﻟﺪﻳﻦ ﻣﺨﺘﺮﻋﺔ ﺗﻀﺎﻫﻲ
ﺍﻟﺸﺮﻋﻴﺔ ﻳﻘﺼﺪ ﺑﺎﻟﺴﻠﻮﻙ ﻋﻠﻴﻬﺎ ﺍﻟﻤﺒﺎﻟﻐﺔ ﻓﻲ ﺍﻟﺘﻌﺒﺪ
ﻟﻠﻪ ﺳﺒﺤﺎﻧﻪ…. ﻳﻌﻨﻲ ﺍﻧﻬﺎ ﺗﺸﺎﺑﻪ ﺍﻟﻄﺮﻳﻘﺔ ﺍﻟﺸﺮﻋﻴﺔ
ﻣﻦ ﻏﻴﺮ ﺍﻥ ﺗﻜﻮﻥ ﻓﻲ ﺍﻟﺤﻘﻴﻘﺔ ﻛﺬﻟﻚ ﺑﻞ ﻫﻲ
ﻣﻀﺎﺩﺓ ﻟﻬﺎ ﻣﻦ ﺃﻭﺟﻪ ﻣﺘﻌﺪﺩﺓ …. ﻣﻨﻬﺎ ﺍﻟﺘﺰﺍﻡ
ﺍﻟﻜﻴﻔﻴﺎﺕ ﻭﺍﻟﻬﻴﺌﺎﺕ ﺍﻟﻤﻌﻴﻨﺔ ﻛﺎﻟﺬﻛﺮ ﺑﻬﻴﺌﺔ ﺍﻻﺟﺘﻤﺎﻉ
ﻋﻠﻰ ﺻﻮﺕ ﻭﺍﺣﺪ ﻭﺍﺗﺨﺎﺫ ﻳﻮﻡ ﻭﻻﺩﺓ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ
ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻋﻴﺪﺍ ﻭﻣﺎ ﺃﺷﺒﻪ ﺫﻟﻚ.(( ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma’ana: ((Bidi’ah wata kirkirarriyar
hanya ce cikin addini mai kama da
addinin gaskiya ana nufin kaiwa
matuka matuka cikin bautar Allah
da yin ta .., ina nufin ita bidi’ah tana
kama da hanyar Shari’ah ba tare
da ta kasance hanyar Shari’ah ta
hakika ba, kai a gaskiya ma tana
karo ne da hanyar Shari’ah ta
fiskoki da yawa … Daga cikinsu
akwai lazimtar wasu irin siffofi
ayyanannu, kamar zikirin da ake yi
a bisa tsarin haduwa a kan sauti
daya’ da kuma rikon ranar
haihuwar Manzon Allah mai tsira
da amincin Allah a matsayin idi, da
abin da yake Kama da haka)).
Intaha.
Sannan Shehu Uthmanu Dan
Fodiyo ya ce cikin littafinsa mai
suna Ihyaaus Sunnah wa Iqmaadul
Bid’ah shafi na 104 :-
(( ﻓﺎﻥ ﻗﻠﺖ ﻣﺎ ﺣﻜﻢ ﻣﺎ ﻳﻔﻌﻞ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻓﻲ ﺷﻬﺮ ﺭﺑﻴﻊ
ﺍﻻﻭﻝ ﻓﻲ ﻳﻮﻡ ﺍﻟﻤﻮﻟﺪ ﺍﻭ ﺍﻟﻴﻮﻡ ﺍﻟﺴﺎﺑﻊ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﻮﻟﺪ ﻣﻦ
ﺍﺟﺘﻤﺎﻉ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻟﻠﺬﻛﺮ ﻭﺍﻟﻄﻌﺎﻡ ﺍﻟﺬﻱ ﻳﻌﻤﻠﻮﻧﻪ ﻟﺬﻟﻚ؟
ﻗﻠﺖ: ﺍﻧﻪ ﺑﺪﻋﺔ ﻣﻜﺮﻭﻫﺔ ﺍﻥ ﺧﻼ ﻋﻦ ﻛﻞ ﻣﻌﺼﻴﺔ.
ﻭﻗﻴﻞ: ﺍﻥ ﺍﻟﺼﻮﺍﺏ ﺍﻥ ﻋﻤﻞ ﺍﻟﻤﻮﻟﺪ ﺍﻟﺸﺮﻳﻒ ﺍﻟﻨﺒﻮﻱ
ﻣﻦ ﺍﻟﺒﺪﻉ ﺍﻟﺤﺴﻨﺔ ﺍﻟﻤﻨﺪﻭﺑﺔ ﺍﺫﺍ ﺧﻼ ﻋﻦ ﻣﻌﺼﻴﺔ .
ﻭﺃﻣﺎ ﻣﺎ ﻳﻌﺘﺎﺩﻩ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻓﻲ ﻫﺬﺍ ﺍﻟﺰﻣﺎﻥ ﻓﻲ ﺫﻟﻚ ﻣﻦ
ﺍﺧﺘﻼﻁ ﺍﻟﺮﺟﺎﻝ ﻭﺍﻟﻨﺴﺎﺀ ﻓﻤﻌﺎﺫ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻥ ﻳﻘﻮﻝ ﺍﺣﺪ
ﺑﺠﻮﺍﺯﻩ.(( ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma’ana: ((Idan ka ce: Mene ne
hukuncin abin da mutane suke yi a
cikin watan Rabii’ul Awwal a ranar
maulidi ko kuwa a ranar bakwai ga
maulidi na taruwar jama’a saboda
yin zikiri da cin abincin da aka yi
tanadinsa saboda hakan? Sai in
ce: Wannan bidi’ah ce
makruuhiyah in yin maulidin ya
wofinta daga dukkan sabon Allah.
Amma kuma wasu sun ce: Abin da
yake daidai shi ne shi bukin
maulidin Annabi yana daga cikin
bidi’o’i masu kyau matukar dai ya
wofinta daga ko wane sabon Allah.
To amma abin da mutane suka
Saba yin shi a maulidi a wannan
zamani na cakuda tsakanin maza
da mata a’uuzu billahi da wani
mutum zai ce halal ne)). Intaha.
Wannan shi ne abin da
malumanmu na mazhabar
Malikiyyah suka fada game da
bukin maulidi.
Sannan Shaikhul Islam Ibnu
Taimiyah wanda ya rasu a
shekarar hijira ta 728 watau
shekaru 706 ke nan da suka wuce
shi ya yi maganar maulidi ya kuma
tabbatar da cewa maulidi bidi’ah
ce, ya rubuta cikin littafinsa mai
suna Iqtidhaa’us Siraa’til Mustaqiim
2/123-124 :-
(( ﻭﻛﺬﻟﻚ ﻣﺎ ﻳﺤﺪﺛﻪ ﺑﻌﺾ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﺍﻣﺎ ﻣﻀﺎﻫﺎﺓ
ﻟﻠﻨﺼﺎﺭﻯ ﻓﻲ ﻣﻴﻼﺩ ﻋﻴﺴﻰ ﻋﻠﻴﻪ ﺍﻟﺴﻼﻡ ﻭﺍﻣﺎ ﻣﺤﺒﺔ
ﻟﻠﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻭﺗﻌﻈﻴﻤﺎ ﻭﺍﻟﻠﻪ ﻗﺪ
ﻳﺜﻴﺒﻬﻢ ﻋﻠﻰ ﻫﺬﻩ ﺍﻟﻤﺤﺒﺔ ﻭﺍﻻﺟﺘﻬﺎﺩ ﻻ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺒﺪﻉ
ﻣﻦ ﺍﺗﺨﺎﺫ ﻣﻮﻟﺪ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﻋﻴﺪﺍ
ﻣﻊ ﺍﺧﺘﻼﻑ ﺍﻟﻨﺎﺱ ﻓﻲ ﻣﻮﻟﺪﻩ ﻓﺎﻥ ﻫﺬﺍ ﻟﻢ ﻳﻔﻌﻠﻪ
ﺍﻟﺴﻠﻒ ﻣﻊ ﻗﻴﺎﻡ ﺍﻟﻤﻘﺘﻀﻲ ﻟﻪ ﻭﻋﺪﻡ ﺍﻟﻤﺎﻧﻊ ﻣﻨﻪ ﻟﻮ
ﻛﺎﻥ ﺧﻴﺮﺍ ﻭﻟﻮ ﻛﺎﻥ ﻫﺬﺍ ﺧﻴﺮﺍ ﻣﺤﻀﺎ ﺍﻭ ﺭﺍﺟﺤﺎ
ﻟﻜﺎﻥ ﺍﻟﺴﻠﻒ ﺭﺿﻲ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻨﻬﻢ ﺍﺣﻖ ﺑﻪ ﻣﻨﺎ ﻓﺎﻧﻬﻢ
ﻛﺎﻧﻮﺍ ﺍﺷﺪ ﻣﺤﺒﺔ ﻟﺮﺳﻮﻝ ﺍﻟﻠﻪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ
ﻭﺗﻌﻈﻴﻤﺎ ﻟﻪ ﻣﻨﺎ ﻭﻫﻢ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺨﻴﺮ ﺍﺣﺮﺹ ﻭﺍﻧﻤﺎ
ﻛﻤﺎﻝ ﻣﺤﺒﺘﻪ ﻭﺗﻌﻈﻴﻤﻪ ﻓﻲ ﻣﺘﺎﺑﻌﺘﻪ ﻭﻃﺎﻋﺘﻪ ﻭﺍﺗﺒﺎﻉ
ﺃﻣﺮﻩ ﻭﺇﺣﻴﺎﺀ ﺳﻨﺘﻪ ﺑﺎﻃﻨﺎ ﻭﻇﺎﻫﺮﺍ ﻭﻧﺸﺮ ﻣﺎ ﺑﻌﺚ .
ﺑﻪ ﻭﺍﻟﺠﻬﺎﺩ ﻋﻠﻰ ﺫﻟﻚ ﺑﺎﻟﻘﻠﺐ ﻭﺍﻟﻴﺪ ﻭﺍﻟﻠﺴﺎﻥ ﻓﺎﻥ ﻫﺬﻩ
ﻃﺮﻳﻘﺔ ﺍﻟﺴﺎﺑﻘﻴﻦ ﺍﻷﻭﻟﻴﻦ ﻣﻦ ﺍﻟﻤﻬﺎﺟﺮﻳﻦ ﻭﺍﻷﻧﺼﺎﺭ
ﻭﺍﻟﺬﻳﻦ ﺍﺗﺒﻌﻮﻫﻢ ﺑﺈﺣﺴﺎﻥ.(( ﺍﻧﺘﻬﻰ .
Ma’ana: ((Haka nan abin da sashin
mutane ke kirkira ko dai saboda
koyi da Kiristoci cikin bukin
Kirsimeti’ ko kuwa saboda son
Annabi mai tsira da amincin Allah
da girmama shi, zai yiwu Allah ya
ba su lada a kan nuna kokari da
soyayya’ amma ba zai ba su lada a
kan bidi’o’in rikon maulidin Annabi
mai tsira da amincin Allah a
matsayin idi ba duk da yake ma
masu tarihi sun yi sabani a kan
wace rana ce da wani wata ne aka
haife shi! Shi dai bukin maulidi
babu wani daga cikin magabata da
ya yi shi duk kuwa da cewa dukkan
dalilan da ake bayarwa na yin
bukin a yanzu akwai su a wancan
lokacin ma, kuma babu wani abu
da zai hana su yin bukin inda yin
shi alheri ne. Lalle ne da yin bukin
maulidi tsantsar alheri ne to da
Salaf Magabata su suka fi
cancantar yin sa a kanmu, saboda
sun fi mu son Manzon Allah mai
tsira da amincin Allah da girmama
shi, kuma sun fi kowa son aikata
alheri. Lalle cikar soyayya da
girmamawa ga Annabi tana cikin
bin shi ne da yi masa da’ah da bin
umurnin shi, da raya sunnar shi ciki
da waje, da yada abin da aka aiko
da shi, da yin jihadi da zuciya, da
hannu, da harshe a kan hakan
wannan ita ce hanyar Magabata na
farko daga cikin Muhajirai da
Ansarawa da wadanda suka bi su
da kyautayi)). Intaha.
Yan’uwa Musulmi! Wannan shi ne
matsayin bukin maulidi daga
bakunan wadannan gagga-gaggan
maluman Musulunci, tare ma kuma
da cewa Maluman tarihi da siiirah
sun yi sabani game da ranar
haihuwar shi Annabi mai tsira da
amincin Allah, a inda wasu suka
ce:
1- An haife shi ne a ran biyu ga
watan Rabii’ul Awwal.
2- Wasu kuwa suka ce an haife shi
ne a ran takwas ga watan Rabii’ul
Awwal.
3- Wasu kuwa suka ce an haife shi
ne a ran goma ga watan Rabii’ul
Awwal.
4- Wasu kuwa suka ce an haife shi
ne a ran goma sha biyumga watan
Rabii’ul Awwal.
5- wasu kuwa suka ce an haife shi
ne a ran goma sha bakwai ga
watan Rabii’ul Awwal.
6- Wasu kuwa suka ce an haife shi
ne a ran ashrin ga watan Rabii’ul
Awwal.
7- Wasu kuwa suka ce an haife shi
ne a ran goma sha biyu ga watan
Ramadhan.
Domin ganin wannan sabanin sai
ku dubi littafin Taariikhul Islam na
Imamuz Zahbii a Juz’in Siirah shafi
na 25-27, da kuma littafin
Albidaayatu wan Nihaayatu na
Alhaafiz Ibnu Katheer 2/662.
Yan’uwa Musulmi! Kauli daidai har
bakwai a kan ranar haihuwar
Annabi mai tsira da amincin Allah
babu kuma wani wanda ya isa ya
ce: wannan kauli shi ne hakikanin
gaskiya wancan kaulin kuma ba
gaskiy ba ne, saboda abu ne da ya
faru kafin zuwan Musulunci kuma
bayan shi Musulunci ya zo bai
tabbatar da ranar haihuwar ba ta
hanyar wahayi saboda rashin
muhimmancin yin hakan a cikin
Addini.
Ke nan ware wata rana daga cikin
ranakun nan da aka ambata da
riyawar cewa ita ce ranar da aka
haifi Manzon Allah mai tsira da
amincin Allah akwai nau’i na karya
da shedan zur a cikin yin hakan.
Allah ya tsare mu da son zuciya.
Wannan shi ne kashi na farko
game da bayananmu a kan bukin
maulidi, kashi biyu na tafe in sha
Allahu Ta’ala, kuma zai yi bayani
ne game da shubuhohin da yan
bidi’ah ke ambatawa domin
tabbatar da bidi’ar maulidi.
Allah Ya nuna mana gaskiya
gaskiya ce ya ba mu ikon bin ta Ya
kuma nuna mana karya karya ce
Ya ba mu ikon kin ta. Ameen.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories