SHEHU UTHMANU DAN FODIO YA CE: MAULIDI BIDI’A CE

Domin neman ƙarin bayani danna nan

Author: Dr. Ibrahim Jalo Jalingo


Babban Malami kuma Mujaddidin Musulunci
Sheikh Uthman Dan Fodiyo ya ce: Maulidi bidi’a
ce abar kyama. Shehu ya rubuta cikin littafınsa
mai suna: Ihyaa’us Sunnah Wa Iqmaadul Bid’ah
shafi na 104 kamar haka:

ربيع الأول
فان قلت ما حكم ما يفعل الناس في )فيشهر
يوم المولد او اليوم السابع من المولد من اجتماع الناس للذكر
والطعام الذي يعملونه لذلك؟ قلت: انه بدعة مكروهة أن خلا
عن كل معصية. وقيل: أن الصواب آن عمل المولد الشريف
النبوي من البدع الحسنة المندوبة اذا خلا عن معصية. وأما ما
يعتاده الناس في هذا الزمان في ذلك من اختلاط الرجال
فمعاذ ال له
والنساء( (.أن يقول احد بجوازه


Ma’ana: ((Idan ka ce: Mene ne hukuncin abin da
mutane suke yi a cikin watan Rabii’ul Awwal a
ranar maulidi, ko kuwa a ranar bakwai ga
maulidi na taruwar jama’a saboda yin zikiri, da
cin abincin da aka yi tanadinsa saboda hakan?
Sai in ce: Wannan bidi’ah ce makruuhiyah in yin
maulidin ya kubuta daga dukkan sabon Allah.
(A wani kaulin kuma) an ce: Abin da yake daidai
shi ne: shirya maulidin Annabi yana daga cikin
bidi’o’i masu kyau da a ake so matukar dai ya
kubuta daga ko wane sabon Allah. To amma
abin da mutane suka Saba yin shi a maulidi a
wannan zamani na cakuda tsakanin maza da
mata A’uuzu Billaahi wani ya yadda da
halaccinsa)
A cikin wannan magana ta Shehu Uthman Dan
Fodiyo za mu fahimci abubuwa muhimmai
kamar haka:

  1. Fatawar Sheikh Uthman Dan Fodiyo ita ce
    Bukin Maulidi bidi’ah ce makruhiya, watau
    bidi’ah abar kyama
  2. Akwai wata magana da ke cewa: Bukin
    Maulidi bidi’ah ce da ake so, to amma shi
    Sheikh Uthman Dan Fodiyo yana ganin wannan
    magana mai rauni ce; wannan shi ne ma ya sa
    ya hikaito maganar da sigar tamriidhi
    Allah muke roko da ya tausaya wa al’ummarmu
    Ya cusa musu kyamatar bidi’ah duk yadda
    Shaidan zai yi kokarin kawata ta cikin
    zukatansu. Ameen.
One response to “SHEHU UTHMANU DAN FODIO YA CE: MAULIDI BIDI’A CE”
  1. umar faruk Abubakar Avatar
    umar faruk Abubakar

    i will like to say a very big jazakumllaah khairan to sheikh may Allaah forgive his short comings and grant him jannahtu firdausi ameen and pray to almighty Allaah to give us too the ability to put more or work like him.

Leave a Reply

Latest updates
Categories