2022 Ramadan Tafseer Cast
This is a dedicated page for 2022 Ramadan Tafseer. The page will be updated regularly.
Sheikh Khamis Al-Misry
Sheikh Bin Uthman Kano English
Sheikh Bin Uthman Kano Hausa
Sheikh Abdurrazak Yahaya Haifan
Sheikh Idris Bauchi Night Tafseer
Sheikh Idris Bauchi Evening Tafseer
Sheikh Ahmad Tunga Al-Azhary
Dr. Mansur Ibrahim Sokoto
Sheikh Rabi’u Rijiyar Lemu
Dr. Sani UmarRijiyar Lemu
Sheikh Musa yusuf Asadussunnah
Sheikh Ahmad Tijjani Guruntum
Sheikh Isa Ali Pantami
Sheikh Tukur Al-Manar
Sheikh Jabir Sani Mai Hula
Dr. Bashir Aliyu Umar
Dr. Abubakar sani Birnin kudu
Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa
Sheikh Mansur Isa Yelwa
Sheikh Abdallah Usman G/Kaya
Sheikh Kabiru Haruna Gombe
027 Sharhin Al-Fur’qan – Sheikh Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo
Huɗuba: Azabar Kabari – Sheikh Mansur Ibrahim Sokoto
001 Fiqhu: Ruwa da rabe rabensa
Bismillahirrahmanirrahim.
Ruwa ya rabu kashi uku gasu kamar haka:
•Ruwa mai tsarƙi mai tsarƙaƙewa: Shine ruwa wanda yake a asalinsa, wanda bai cakuɗu da wani abu ba, najasa ko ba najasa ba. Kamar ruwan Kogi, Rijiya, Sama, kududdifi da makamantansu. Duka irin wa’innan ruwa masu tsarƙi ne, ana iya shansu, sannan kuma ana iya yin aikin Ibada dasu.
•Ruwa mai tsarƙi wanda baya tsarƙaƙewa: Shine ruwa wanda ya cakuɗu da abu mai tsarƙi. Kamar ruwan da ya cakuɗu da Siga, ko gari. To wannan ruwa Mai Tsarki ne a karan kansa amma kuma baya tsarkake wa, ma’ana za’a iya shan ruwan, ko kuma ayi aikin gida dashi, amma baza’ayi aiki na ibada dashi ba, kamar alwala ko wankan janaba da makamantansu.
Read More…Hukuncin Magana yayin Hudubar Juma’a
Tambaya: Shin ya halatta mutum yayi magana yayin Hudubar Liman?
Amsa: Baya halatta mutum yayi magana yayin hudubar liman.
Dalili: Allah madaukakin sarki yace:
Idan aka karanta Al-Qur’ani Ku saurara, sannan kuyi shiru
Suratul-Aaraf: 204
Imam Ahmad yace:
Maluma da yawa sun tafi kan cewa wannan ayah ta sauka ne kan Sallah da kuma Khudbah
Fathul Bari: 5/499
Dalili na Biyu: Abu Huraira ya rawaito daga Annabi Sallallahu alaihi wasallama yace:
Idan kace wa Abokinka ranar Juma’a kayi shiru alhali liman yana khudbah toh kayi lagawu(Yasasshen zance)
Bukhari: 934
Muslim: 851
Wannan Hadisi yana nuna haramcin magana a yayin khudubar Liman, sabida in ya zamto Cewa da zakayi wa Abokin zamanka yayi shiru laifi ne duk da cewa kana Umarni ne da kyakkyawa ashe magana wanda ba wannan ba shi yafi kasance wa Haramun.
Abin Lura: Baya halatta Wanda yaje masallacin Juma’a yayi magana yayin hudubar Liman, koda ko yaga wani yana magana ba zai hanashi a wannan lokaci ba, sai dai ya bari in Liman ya kammala huduba.
Baya Halatta ga Musulmi yayi nema kan neman dan’uwansa
Addinin Musulunci a koda yaushe yana kokari wurin dakile duk wata tsabani da rashin jituwa tsakanin Mabiyansa, shiyasa a wurare da dama Allah da Manzonsa suka hana mu yin tsabani da rarrabuwa kamar yadda Allah yace:
Kuyi Biyayya ga Allah da Manzonsa, kada kuyi jayayya sai kusamu rauni, sannan karfin ku ya tafi.
Suratul Anfal Ayah: 46
Sabida Hakane ma Annabi Sallallahu alaihi Wasallama ya hana Mutum musulmi yayi nema kan neman dan’uwansa Musulmi. Annabi Sallallahu Alaihi wasallama yace:
Kada mutum yayi nema akan neman dan’uwansa
Bukhari: 5144
Muslim: 1413
Wannan Hadisi a bayyane yake cewa haramun ne mutum yasan cewa Dan’uwansa Musulmi yana neman auren wata, kuma iyayenta da ita sun amsa mishi sa’annan kuma yaje shima ya shiga nemanta. Sai dai idan bata amsa mishi ba, toh anan zai iya zuwa ya nema har sai ta tsayar da wadda takeso a tsakaninsu.
Abin Lura: Idan har ya zamto bata amince da wanda ya fara zuwa wurinta ba to ya halatta ga na biyun yaje ya nemi aurenta,
Haka nan idan shi na farkon ne ya janye ko kuma yayi izini wa na biyun yaje ya neme ta to anan babu laifi.
Allah yasa mudace.
Falalar Rakao’i biyu na Alfijr
Annabi Sallallahu alaihi wasallama yace
“Rakao’i biyu na alfijr yafi duniya da abinda ke cikin ta alheri”
Ana yin wannan rakao’i biyu ne bayan ketowar alfijir kafin Sallar asubahi.
Kuma Annabi ya kasance baya barin wannan raka’oi biyu a kowani irin yanayi.
yana gida ko yana tafiya.
Allah yasa mudace.
Idan Ka zabi mace mai addini ka aura ka rabauta
Da sunan Allah mai rahama mai jin kai.
Kowani na miji akwai abinda yake jan hankalinsa wurin auren mace, mafi shahara daga cikin wa’innan sabuba sune kamar haka:
- Kyawu
- Dukiya
- Dangi
- Addini
Wa’innan abubuwa sune mafi yawan abubu wa da suke jawo hankalin na miji ya auri mace.
Read More…Neman sani kafin aiki da amfani da lokaci wurin neman ilimin addini
Shin ka taba zama kayi tunani meyasa Allah ya halicce ka? Kuma shin ko kana gudanar da rayuwar ka wurin cimma wannan abinda Allah ya halicce ka don shi?
Shin a cikin awa 24 da kake dashi a rana awa nawa kabai wa Abinda aka halicce ka don shi?
Allah ya halicce mu ne don mu bauta masa, kuma ba’a bauta masa da jahici,
Kamar yadda yayi bayani