KIRA ZUWA GA TAFARKIN MAGABATA NA KWARAI (Manhajus Salafis Salih) *** 34(Sheikh Aliyu Said Gamawa)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

KARANTARWAR SHEHU USMAN
DAN FODIYO A KAN BIN SUNNAH
(1)
Kamar yadda magabatan farko da
manyan malaman Sunnah suka
daidaita wajen tsayuwa a kan
tafarkin Manzon Allah (S.A.W.),
haka suka dage wajen isar da
wannan saqo. A cikin wadannan
magabata akwai Mujjadadi Sheikh
Usman dan Fodiyo wanda ya yi wa
Sunnar Manzon Allah (S.A.W.)
hidima, ya kuma yi fada sosai da
bidi’o’i da suka mamaye al’ummar
Musulmi na zamaninsa. Ya yi
rubuce-rubuce masu yawa a
wannan fanni, cikinsu akwai wani
littafinsa mai suna “Hidayatud-dull
ub” ya kawo mas’aloli guda goma
da suka shafi riqo da Sunnar
Manzon Allah (S.A.W.) kamar
haka:
1. Sanar da Almajirai cewa duk
abin da ya zo daga Sunnar Manzon
Allah (S.A.W.) ba za a kira shi
Mazhabar kowa ba. Wajibi ne
kuma a kan kowa ne Musulmi ya yi
aiki da shi, kuma wajibi ne a karbi
kiran duk wanda ya yi kira zuwa ga
wannan abu.
2. Allah bai wajabta wa kowa ba a
cikin LittafinSa, haka kuma Manzon
Allah (S.A.W.) bai wajabta wa
kowa ba a cikin Sunnarsa, cewa
tilas ne mutum ya kama wata
mazhaba ayyananniya. Da a ce su
magabatanmu sun yi haka da kuwa
sun afkar da mutane cikin zunubi,
domin da sun hana yin aiki ke nan
da duk wani Hadisi wanda shi
Mujtahidin nan mai Mazhaba bai
same shi ba.
An yi tambaya, ko wajibi ne a kan
dukkan Mutum wanda bai kai ga
darajar zama Mujtahidi ba, ya kama
mazhaba guda ayyananniya ya
lazimce ta?
A wajen wajibi an kawo ra’ayi biyu.
Na farko an ce yana lazimta kamar
yadda marubucin littafin Jam’uj
Jawami’i ya ingantar da wannan
magana. Ra’ayi na biyu kuwa ya
ce, a’a ba ya lazimta, kuma
wannan Annawawi ya zaba.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories