Fatawa A Kan Qunuti Domin 'Yan Uwanmu Musulmin Yobe da Borno da Adamawa da Afrika ta Tsakiya(Dr. Mansur Sokoto)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Assalamu alaikum ‘yan uwa musulmi
Dukkanmu muna sane da halin da ‘yan uwanmu musulmi suke ciki a jihohin da ke Arewa maso gabascin Najeriya da kuma yan uwanmu musulmi na Afrika ta tsakiya. Babu shakka suna cikin halin damuwa kwarai. Ana kisan su kamar kiyashi, ana tozarta iyalansu, ana maraitar da ‘ya’yansu. Wannan yana wajabta mana taimaka ma su da addu’a. Kasancewar sunnah ta zo da yin addu’ar kunuti a irin wannan hali muka ga ya dace mu yi wa ‘yan uwa bayani a kan addu’ar da hukunce-hukuncenta bisa ga sunnah don mu yi aiki da ita saboda taimakon ‘yan uwanmu. Idan an taba wadannan jihohi a yau gobe ba mu san in da za a taba ba.
Mun yi wannan fatawa a watan Mayu na shekarar bara, a wannan karon kuma muna goyon bayan kungiyar Jama’atu Nasril Islam a kan kiran da ta yi ma limamai su yi wannan kunuti. Muna fatar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatis Sunnah ita ma za ta bi sahun masu wannan kira. Haka ma sauran kungiyoyin musulmi a wannan kasa da makwabtanmu.
Ga bayanan da ya kamata mu sani a kan wannan addu’a:
1. Wannan addu’a ana kiran ta “Qunutun Nawazil” kuma ana yin ta ne a lokacin da wasu musibbu suka sauka ga wasu musulmi. Ana kuma yin ta ne a dukkan sallolin farilla.
Ya tabbata daga hadisin Anas bin Malik (RA) cewa Annabi (SAW) ya yi wata daya yana kunuti yana la’antar kabilun Ri’il da Zakwan da Usayya da Banu Lihyan saboda sun yaudare shi; sun kashe sahabbansa saba’in mahardatan Alkur’ani.
2. Qunutin ana yin sa ne a raka’ar karshe bayan tasowa daga ruku’i kamar yadda sayyidina Abu Huraira (RA) ya ruwaito Annabi (SAW) ya yi a lokacin da kafiran Makka suka rike wasu musulmi masu rauni suka hana su yin hijra.
3. Wanda yake sallah shi kadai zai iya yin kunuti. Haka shi ma liman zai yi shi a bayyane – a dukkan salloli – kuma masu bin sa suna cewa “Amin” kamar yadda Ibnu Abbas (RA) ya ruwaito. Abu Dawud ya ruwaito shi kuma Nawawi da Ibnul Qayyim sun inganta shi.
4. Ba a tsawaita kunutin kamar yadda sayyidina Anas (RA) ya fada. Kuma ba a yin wasu addu’oi sai addu’ar da dalilinta ya kama, sannan ba a rufe shi da salati irin yadda ake rufe kunutin witri kamar yadda wasu sahabbai ke yi.
5. Ana ci gaba da yin kunutin har Allah ya kawar da matsalar da ta sa ake yin sa. Zadul Ma’ad naIbnul Qayyim (1/272).
6. Duk da yake a wurin sujuda addu’a ta fi kadari amma an ce ayi “Qunutun Nawazil” a bayan ruku’i. Hikimar ita ce, samun cewa “amin” daga masu bin liman sallah. Kuma shi ya sa ake yin ta a bayyane ko da a sallolin wuni. Fathul bari (2/570).
7. Ana daga hannuwa a cikin wannan kunutin kamar yadda Baihaqi ya ruwaito a cikin Sunan (2/212).
8. Ana iya yin amfani da addu’ar manzon Allah (SAW) sai a shigar da bukatar da ake kunuti a kan ta. Misali, ana iya cewa:
“اللهم أنج إخواننا المسلمين في بورنو، اللهم أنج إخواننا المسلمين في يوبي، اللهم أنج إخواننا المسلمين في أدماوا، اللهم أنج إخواننا المسلمين في إفريقيا الوسطى، وفي كل مكان، اللهم احقن دماءهم، اللهم انصرهم ، واشدد وطأتك على من ظلمهم وقاتلهم، ومن شايعهم وأعانهم يا قوي يا عزيز”.
Ko kuma ayi amfani da addu’ar Qunutin sayyidina Umar (RA) lokacin da yaki ya tsananta tsakanin sa da Nasara. Sunan Al-Baihaqi (2/210) da Irwa’ul Galil na Albani (2/170).
“اللهم إنا نستعينك ونؤمن بك، ونتوكل عليك، ونثني عليك الخير، ولا نكفرك، اللهم إياك نعبد، ولك نصلي ونسجد، وإليك نسعى ونحفد، نرجو رحمتك ونخشى عذابك، إن عذابك الجدَّ بالكفار مُلحق، اللهم انصر إخواننا المسلمين في برنو وأدماوا ويوبي، اللهم نج المسلمين في إفريقيا الوسطى، وفي كل مكان، اللهم احقن دماءهم وفُكّ أسرهم، وتولّ أمرهم، وارحم موتاهم، وكن لهم عونا ونصيرا في أراملهم وأيتامهم يا ذا الجلال والإكرام”
9. Ba a shafa fuska bayan gama kunuti domin bai zo a Sunnah ba kamar yadda Imamun Nawawi ya fada. Al-Majmu’u na Nawawi (3/490).
10. Ba a yin sa a sallar jum’ah saboda shi ma bai tabbata ba a cikin Sunnah. Kuma wasu daga cikin sahabbai sun hana. Musannaf na Abdurrazzaq (3/194) da Musannaf na Ibn Abi Shaibah (2/46).
11. Idan liman bai yi kunuti ba Mamu ba zai yi ba saboda Annabi (SAW) ya ce, “Kada ku saba ma limamanku”. Majmu’u Fatawa Ibn Taimiyya (23/115-116)
Allah ya sa mu dace. Allah ya kawar da fitina daga kasarmu da sauran kasashen musulmi. Allah ya hada kan musulmi a kan gaskiya.
Wassalamu Alaikum Warahmatullah
Daga Kwamitin Da’awa Na Cibiyar Sahabbai, Sokoto.
29 ga R. Akhir 1435H (1/3/2014)
Ina fatar ku yi sharing wannan fatawa don gamewar ta ga sauran musulmi.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

3 responses to “Fatawa A Kan Qunuti Domin 'Yan Uwanmu Musulmin Yobe da Borno da Adamawa da Afrika ta Tsakiya(Dr. Mansur Sokoto)”
  1. Nura yusuf Avatar
    Nura yusuf

    Ass/m, babu abun da zance daku sai dai Allah yasaka muku da alcairi ya kuma kareku daga sharrin ma su sharri, amee

  2. Misbah Avatar

    Allah ya saka da alkhairi.

  3. Fa'iz Ibrahim Jibia Avatar
    Fa’iz Ibrahim Jibia

    JAZAKUMULLAHU KHAIRA

Leave a Reply

Latest updates
Categories