ABIN DA MUSULMI ZAI CE A LOKACIN DA JINJIRIN WATA(Dr Ibrahim jalo Jalingo

Danna nan domin shiga group na karatu Online

‘yan’uwa Musumi! Mun gode Allah
da ya nuna mana wannan yini na
30 ga watan Sha’aban, muna
kuma rokonSa Madaukakin Sarki
da Ya nuna mana watan Ramadan
mai kamawa nan da ‘yan awowi
kada. Ameen.
********************************
Sannan muna jan hankalin
Yan’uwa da cewa in Allah Ya kai
mu yammaci can an jima, mu ka
ga jinjirin watan Ramadan, toh sai
mu yi addu’a a lokacin da muka
gan shi, saboda ya tabbata a cikin
Sunnah cewa Annabi mai tsira da
amincin Allah in ya ga jinjirin wata
ya kan yi addu’ah.
Imamut Tirmizii ya ruwaito hadithi
na 3,451, daga Dalhatu Dan
Ubaidullah cewa Annabi mai tsira
da amincin Allah ya kasance in ya
ga jinjirin wata sai ya ce: ((Ya
Allah! Ka tsayar mana da shi tare
da Jin dadi, da Imani, da
Amintuwa, da Musulunci.
Ubangijina da Ubangijinka Allah
ne)). Albaanii ya inganta shi.
Ga yadda addu’ar take da Larabci:-
(( ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺍﻫﻠﻪ ﻋﻠﻴﻨﺎ ﺑﺎﻟﻴﻤﻦ ﻭﺍﻻﻳﻤﺎﻥ ﻭﺍﻟﺴﻼﻣﺔ
ﻭﺍﻻﺳﻼﻡ ﺭﺑﻲ ﻭﺭﺑﻚ ﺍﻟﻠﻪ)).

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories