Hukuncin Magana yayin Hudubar Juma’a

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Tambaya: Shin ya halatta mutum yayi magana yayin Hudubar Liman?

Amsa: Baya halatta mutum yayi magana yayin hudubar liman.

Dalili: Allah madaukakin sarki yace:

Idan aka karanta Al-Qur’ani Ku saurara, sannan kuyi shiru

Suratul-Aaraf: 204

Imam Ahmad yace:

Maluma da yawa sun tafi kan cewa wannan ayah ta sauka ne kan Sallah da kuma Khudbah

Fathul Bari: 5/499

Dalili na Biyu: Abu Huraira ya rawaito daga Annabi Sallallahu alaihi wasallama yace:

Idan kace wa Abokinka ranar Juma’a kayi shiru alhali liman yana khudbah toh kayi lagawu(Yasasshen zance)

Bukhari: 934
Muslim: 851

Wannan Hadisi yana nuna haramcin magana a yayin khudubar Liman, sabida in ya zamto Cewa da zakayi wa Abokin zamanka yayi shiru laifi ne duk da cewa kana Umarni ne da kyakkyawa ashe magana wanda ba wannan ba shi yafi kasance wa Haramun.

Abin Lura: Baya halatta Wanda yaje masallacin Juma’a yayi magana yayin hudubar Liman, koda ko yaga wani yana magana ba zai hanashi a wannan lokaci ba, sai dai ya bari in Liman ya kammala huduba.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories