Hukuncin Shan Rubutu

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Tambaya: Shin ya Hallatta Mutum ya rubuta ayar Alqur’ani a Allo ya wanke ya sha?

Amsa: Babu laifi game da rubuta Ayar Al-Qur’ani a allo ko a jikin wani abu mai tsarki, sannan a sha, ko kuma a shafa shi awurin da yake yi wa mutum ciwo. Domin an rawaito haka daga magabata.

Imam Ibnul Qayyim lokacin da yake magana game da Ruƙya ta Kambun baka yace:

Wasu daga cikin magabata suna ganin cewa a rubuta wa wanda kambun baka ya same shi ayoyi na Al-Qur’ani sannan a bashi yasha, Mujahid yace: babu laifi ya rubuta Alkur’ani ya shayar dashi ga mara lafiya.

Zaadul ma’ad: 4/170

Haka nan an rawaito wannan aiki daga magabata kaman su Abi ƙilaba, da Ibnu Abbas yayi umarni a rubuta wa wata mace Ayoyi na Alqur’ani lokacin da ta samu wahala wurin haihuwa.

Yazo acikin fatawa ta Lajnatud-da’imah:

Karanta Alqur’ani ko Hadisi wa mara lafiya a tofa masa tabbatacce ne acikin Sunnar Annabi Sallallahu alaihi Wasallama, Annabi yayi wa kansa, sannan kuma yayi wa wasu daga cikin Sahabban sa, amma rubuta Ayar Alqur’ani da tawada ko makamantansa sannan a wanke da ruwa a sha, ko karanta Ayar Al-Qur’ani akan zuma da nono da makamantansu da shafawa a jiki tare da haɗa shi da Almiski babu laifi akan hakan, Magabata na gari sunyi hakan.

Fatawa Lajnatud-da’imah: 1/97

Halaccin Rubuta ayoyin Alkur’ani da kuma sha shine fatawar Sheikh Bin Baz Allah yayi masa Rahama. A duba Fatawa Islamiyya: 1/30

Wannan game da Ayoyin Alqur’ani da Hadisan Annabi Sallallahu alaihi Wasallama, duk ana iya rubuta su a sha, Musamman Hadisai da suka ƙunshi addu’oi.

Amma baya halatta mutum yasha Hatimi, ko wani rubutu wanda baisan asalinsa ba, ko kuma wanda ke ƙunshe da shirka da Allah. Irin Wanda za’a ce yana kawo farin jini, ko makamantansu, duka wannan bai halatta ba, domin bashi da Asali a Addini.

Sannan Sheikh Bin Baz bayan da ya amsa tambayar da akayi masa game da hukuncin shan Rubutu sai yace:

Abinda yafi falala shine Mutum ya karanta ya tofa wa kansa ko waninsa, yafi fiye da rubuta wa.

Sabida Haka aka Rawaito Annabi Sallallahu alaihi Wasallama yana yi.

Allah shine mafi sani.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories