Shin ya Halatta Mutum ya karanta Zikirin Safe da Yamma ko Alqur’ani a kwance?

Tambaya: Meye Hukuncin Karanta Alqur’ani ko Yin Zikiri a kwance?

Amsa: babu laifi mutum ya karanta Alqur’ani ko Zikiri a kwance.

Dalili: An rawaito daga A’ishah Allah ya ƙara mata yarda tace:

Annabi Sallallahu Alaihi Wa Sallam ya kasance yana kishingiɗa a wata Riwaya yana kwantar da kansa a Jiki na ta gaba alhali yana karanta Alqur’ani

Sahihul Bukhari: 297

Wannan Hadisi yana nuna halaccin Karatun Alqur’ani a kwance ko a kishingiɗe. Sannan babu laifi mutum ya karanta Alqur’ani yana jingine da iyalinsa koda kuwa tana Jinin Al’ada ne.

Allah shine mafi sani.

Click Here to Support our work

Leave a Reply

%d bloggers like this: