KIRA ZUWA GA TAFARKIN MAGABATA NA KWARAI (Manhajus Salafis Salih) *** 32(Sheikh Aliyu Said Gamawa)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

BANBANCIN DA KE TSAKANIN
SHUGABANNIN MAZHABOBI WAJEN
HANYOYIN DA SUKE DOGARA DA
SU (5)
TSARIN IMAMUAHMAD
BIN HAMBALI
Shi kuwa Imamu Ahmad Bin
Hambali qa’idojin mazhabarsa
suna da kusanci qwarai da
qa’idojin mazahabar Imamu
Shafi’iy, wanda bayaninta ya
gabata. Saboda haka yana tabbatar
da hukunci ta hanyar riqo da
wadannan ginshiqai a kan jerin da
aka rattaba kamar haka:
1. Nassoshi daga A1-Qur’ani da
Sunnah, wadanda idan ya same su
ba ya waiwayar waninsu, kuma ba
ya gabatar da wani abu da ya
danganci aikin mutanen Madina,
ko ra’ayi ko qiyasi ko maganar
Sahabi ko Ijma’i wanda ya ginu a
kan rashin sanin wanda ya saba da
shi, wato ba ya gabatar da kowane
daya daga wadannan abubuwa a
kan Hadisi sahihi marfu’i.
2. Idan bai samu nassi game da
mas’ala ba, sai ya koma ga fatawar
Sahabbai. Idan ya sami magana ta
wani Sahabi wadda ba a san wani
Sahabi da ya saba kan maganarsa
ba, to ba zai tsallake zuwa ga wani
abu dabam ba, ba kuma zai
gabatar da wani aiki ko ra’ayi ko
qiyasi a kan wannan magana ba.
3. Idan Sahabbai suka yi sabani,
sai ya dubi maganar tasu ya zabi
wadda ta fi kusa da A1-Qur’ani da
Sunnah, kuma ba zai fita daga
maganganun nasu ba. Idan kuma
bai gano wata magana da ta fi
kusa da A1-Qur’ani da Sunnah ba,
sai ya hikaito sabanin nasu amma
ba zai nuna maganar da ya zaba a
kan ta sauran ba.
4 Hadisi mursali da Hadisi mai
rauni wanda ake iya magance
raunin nasa don bai sami wata
madogara ba a wannan babi banda
shi, ko kuma wani da shi, kuma
yana gabatar da irin wannan Hadisi
a kan qiyasi.
5. Qiyasi wanda a wajen Imamu
Ahmad din dalili ne na larura da
ake komawa gare shi a lokacin da
ya rasa daya daga hujjoji da suka
gabata.
6. Toshe kafar barna. (saddud
zara’i’i)

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories