KIRA ZUWA GA TAFARKIN MAGABATA NA KWARAI (Manhajus Salafis Salih) *** 35(Sheikh Aliyu Said Gamawa)

Domin neman ƙarin bayani danna nan

KARANTARWAR SHEHU USMAN
DAN FODIYO A KAN BIN
SUNNAH (2)
Ci gaba …
4. An yi tambaya, shin ko ya
halatta ga wanda ya riga ya
kama wata mazhaba
ayyananniya ya fita daga gare ta?
A wajen jawabi an ce, “Na’am,”
zai iya fita yanke. Rafi’i shi ne ya
inganta wannan ra’ayi. Ko da
yake wani qaulin an ce ba zai iya
fita yanke ba, domin ya riga ya
daure kansa. A qauli na uku
kuwa aka ce bai halatta ya fita da
wadansu mas’alolin mazhaba ba,
sannan ya ci gaba da riqo da
wasu mas’alolin.
5. Duk Mujtahidi da ya sava wa
nassin Alqur’ani da Hadisi ko
Ijma’i, ba za a bi shi ga wannan
magana ba.
6. Duk abin da almajiran
mujtahidi suka fahimta daga
maganar mujtahidin nan ba za a
lissafa da shi ba a cikin
mazhabarsa. Amma daga baya,
sakacin mutane ya yi yawa har
suka riqa jingina ra’ayoyin masu
wallafar littafi da masu yi wa
littafi sharhi ga mazhabar
wadanda suke koyi da shi, suka
mai da su kamar ra’ayoyin
mujtahidin nan na asali. Sai daga
qarshe al’amari ya koma ga su
almajiran suna koyi da ratayawa
da junansu. Ta haka har ya zama
kowane littafi ya kai Juz’i ashirin,
alhali kuwa ainihin maganar
mujtahidin a cikinsa idan an tara
ba za ta kai Juz’i daya ba.
Wajibi ne a kan kowane Musulmi
mukallafi ya qudurta cewa
dukkan Imaman Musulmi a kan
shiriya ta Ubangijinsu su ke.
(Wato ba sa cikin bata). Wato su
Imamu Abu Hanifa, Maliki,
Shafi’i da Imamu Ahmad bin
Hambal.
8. Wajibi ne a kan kowane
Musulmi Mukallafi kada ya yi
qyamar aiki da maganganunsu
(Mujtahidan). Wadansu mutane
a yau sun kasance idan waninsu
ya yi amfani da maganar da ba
ta Imaminsa ba, sai ya ce, “Bari
in yi koyi da shi don larura.”
Watau ya yi aiki da hukuncin a
kan hukuncin larura wadda take
halartar da abin da aka hana. Sai
ya ga kamar dai ya afka ne a
cikin zunubi. To ya sani cewa
wannan aiki nasa da ya yi na
qyamar hukuncin Mujtahidin
nan, shi ne babban zunubi
wanda ya wajaba ya tuba saboda
aikata shi, kuma ya nemi gafara
a wurin Allah. Domin da su irin
wadannan mutane sun yar da
cewa dukkan Imaman
Musuluunci a kan shiriya su ke,
da ba su yi qyamar aiki da
magabatansu ba, domin shiriya
ba a qyamar ta matuqar dai an
tabbata ita ce.
9. Duk wanda ya bar aikin da aka
yi sabani a kan zamowarsa
wajibi, ko kuwa ya aikata abin da
aka yi sabani a kan zamowarsa
haram, to ba za a yi masa inkari
ba, idan har ya dogara da qaulin
malami. Sai fa idan ya dogara ga
maganganunsa wadanda suka
saba wa nassin Alqur’ani da
Sunnah ko Ijma’i. Amma
matuqar aikinsa ya yi daidai da
wata maganar Mujtahidi na
Alhalus-Sunnah, to ba za a yi
masa musu ba. Amma da a ce
an yi musu shi ne a ce abin da
wannan mutum ya yi haram ne.
Amma da a ce an yi musu ne da
nufin shiryarwa ko don yi masa
nasiha, to shi wannan ba za a
kira shi inkari ba. Amma a wajen
babin fatawa, malamin da ke yi
wa mutane fatawa da wani qauli
manisanci ga hankali, ko kuma
mai raunin hujja, ya bar
mashahuriyar magana mai
qarfin hujja, to za a iya yi masa
inkari domin bai halatta a yi
fatawa ba sai da mashahuriyar
magana mai qarfi.
10. Mutum wanda za a yi wa
inkari na hukunci, shi ne wanda
ya sava wa nassin Alqur’ani da
Sunnah ko na Ijma’i.
Wannan bayani na Shehu
Usmanu dan Fodiyo ya nuna
mana irin tsarin karantarwar
Shehun Malamin. Sannan za mu
fahimci cewa riqo da mazhaba
guda daya ba tilas ba ne cikin
addinin Islama. Haka kuma riqo
da mazhabar ba laifi ba ne, sai
dai in ka yi watsi da maganar
Manzon Allah (S.A.W.)
ingantacciya don riqo ko bin
jagoran mazhabar, to a nan kam
an kauce wa karantarwar Annabi
(S.A.W.) da Sahabbai da sauran
magabata na qwarai har da shi
jagoran Mazhabar da kake bi
din. Domin dukkansu sun ce in
an ga Hadisi ingantacce ya sana
da fatawa ko karantarwarsu to a
ajiye maganarsu a dauki ta
Manzon Allah (S.A.W.) ita ta fi
daidai (Wallahu A’alamu).

Leave a Reply

Latest updates
Categories