Ramadaniyyat: Ramadaniyyat: 1445 [1]‎ Rabbaniyyun: Ilimi da Malanta:‎

Danna nan domin shiga group na karatu Online

0.‎ Gabatarwa:‎

0.1‎ Malanta, kamar kowace irin sana’a a rayuwan ɗan’adam, ‎akan samu ƙwararru waɗanda suka san sana’arsu ciki da waje, suke kuma ‎kula da ita suna tsare mata mutunci. Hakanan akan kuma samu bara-gurbi ‌‎’ya shisshigi a cikinta, waɗanda suka yiwo kutse da taka-haye. Sai dai ‎samuwar ‘yan take-haye a cikin sha’anin malanta abu ne mai matuƙar ‎haɗari a ruyuwar al’umma, domin varnarsu ba za ta taƙaita a kan gangar ‎jiki kawai ba, a’a, za ta tavo har zukata, ta kuma yi mungun ta’adi a addini ‎mutum. Yawan waɗannan bara-gurbin malaman ya jefa mutane dadama ‎cikin ɗimiwa da ruɗani har sun kasa tantance tsakanin ‘yan gaske da kuma ‌‎’yan gangan.‎

‎0.2‎ Babu mamaki a samu bara-gurbi a cikin rukunin malamai ‎duk kuwa da kasancewar sana’arsu sana’a ce ta masu neman lahira da ‎yardar Allah, saboda malamai su ne magada annabawa, to amma kuma ‎har a tarihin annabta an samu ‘yan tamore maƙaryata waɗanda suka yi ‎da’awar annabta ba tare da hujja ba.

‎0.3‎ Tun a ƙarshe-ƙarshen rayuwar Annabi (SAW) aka samu al-‎Aswad al-Ansi wanda ya yi da’awar annabata, kuma ya ja zugar ‎mabiyansa har suka mamaye wani vangare na ƙasar Yaman, ‎kafin Allah ya ba wa Musulmi nasarar gama wa da shi, bayan ‎sun sami haɗin kan matarsa wadda ya tursasa mata auren sa ba ‎tare da tana son sa ba. Hakanan aka samu Ɗulaihatu al-Asadi ‎wanda shi ma ya yi da’awar annabata, Khalid ɗan Walid ya yi ‎arangama da rundunansa, ya kuma yi nasarar karya lagonsa, ‎amma daga bisani sai ya dawo Musulunci ya fita yaƙe-yaƙe tare ‎da Musulmi har ya yi mutuwar shahada a Nahawand. Sannan ‎kuma an yi irin su Musalima al-Kazzab, shi ma haka ya bushi ‎iska ya kira kansa annabi, Musulmi suka yaƙe shi tare da ‎mabiyansa, suka yi kuma nasarar muruƙushe ta’addancinsa, ‎Wahshi ya kashe shi murus har lahira, tasa ta zo ƙarshe.

‎0.4‎ To haka nan aka ci gaba da samun masu da’awar annabata na ‎ƙarya, waɗanda suka riƙa ruɗar wasu makakkun mutane masu ‎gaskata su. To idan har an samu irin wannan shisshigi a cikin ‎sha’anin annabta, to ka ga babu wani mamaki a samu irinsu da ‎yawa a cikin malamai, domin malamai su ne magada annabawa. ‎Da jimawa Imam Auzai ya tava cewa, “Wannan ilimi ya kasance ‎abu ne mai daraja, mutane suna koyon sa daga junansu, to yayin ‎da ya shiga cikin littattafai, sai waɗanda ba ahalinsa ba suka ‎kutsa kai cikinsa”. [Ibn Salah, sh. 182, 183]. To tun daga ‎wannan lokaci ne, wato ƙarni na biyu bayan hijira, matsalar ‎malantar gangan da taka-haye ta samo asali. ‎

‎0.5‎ Ibn Hazm yana faɗa cewa, “Babu abu mai cutar da ilimi da ‎malanta kamar ‘yan shisshigi a cikinta, domin su ne suke yaɗa ‎jahilci da sunan ilimi, suna kuma varna amma suna zoton gyara ‎suke yi”. [Ibn Hazm, Mudawat an-Nufus, sh. 23].‎

Za mu ci gaba da tattauna wannan matashiya ta Ilimi da malanta a ‎tsawon kwanakin Ramadan masu albarka in sha Allah.‎

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories