INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!!! SHIN KUNSAN MUMMUNAN BALA'IN DAKE FUSKANTARMU KUWA???

Danna nan domin shiga group na karatu Online

INNALILLAHI WA’INNA ILAIHI RAJI’UN!!!
SHIN KUNSAN MUMMUNAN BALA’IN DAKE FUSKANTARMU KUWA???
Ga Abinda Voa Hausa suka posting…
Shugaba Goodluck Jonathan na Najeria na neman agajin kasa da kasa domin yakar Boko Haram, saboda a cewarshi kungiyar barazana ce ga Afirka da duniya ma baki daya. Me kuka gani?
Hazbunallahu wani’imal wakeel… Meye wannan ke nunawa Ya Al’ummar Manzon Allah(saw)…? Wannan ba karamar bala’I bace wadda bamusan karshenta ba. Shin ina musulmanmu sukene? Shin kunsan me wannan maganar take nufi?
Shugaban kasanku yana neman agajin kasa da kasa su taimakeshi yaki da ‘yan boko haram…
Shin wannan ba yunkurine na ruguza musulmai ba? Shin in akazo yaki da boko haram dinnan a’ina za’a jibge sojojin da sukazo yakin? A arewa!!! Shin Yana nufin duk hukuman dake Nigeria boko haram sunfi karfinsu kenan,? amma ya iya tura sojoji mali? Shin ma suwanene wa’innan ‘yan boko haram din? Ina mutanen da akace ankama da sunan boko haram meyasa baza’ayi bincikesu a tabbatar dasu wayeba?
Ya dace malumanmu da shuwagabanninmu suyi tunani suyi kira zuwa ga gwamnati ta janye wannan mummunan manufa tasu, domin wallahi inmuka yadda muka bari wa’innan azzalumai ja’irai mayu ‘yan ta’adda turawan yamma suka shiga wannan kasan namu toh wallahi abinda ke faruwa a iraqi mukeji a labarai shi zai fara aukuwa akanmu….
Mu babu wani ‘yan boko haram acikinmu, ‘yan boko haram sunanan acikin gwamnati kuma gwamnati ta sansu, domin shi shugaban kasa da kansa ya tabbatar wa duniya cewa yasan su waye ‘yan boko haram. Toh meyasa baza’a tuhumeshi ya bayyanasu ba? Sarakuna, shuwagabanni malamai, ku tashi tsaye ku hana wannan mummunar bala’I shigowa wannan kasa taamu inba haka ba wallahi sai Allah ya tambayeku… Allah karemu da sharrin Azzalumai munafukai ‘yan ta’adda masu son shan jinin al’ummah…

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

One response to “INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN!!! SHIN KUNSAN MUMMUNAN BALA'IN DAKE FUSKANTARMU KUWA???”
  1. Ahmad Yusuf Assqalaini Avatar
    Ahmad Yusuf Assqalaini

    Allah ya sakama da alkhairinsa, amma wadannan sarakan da maluman dake kira garesu ai karnukan farautarsune, wasu kuma storo ke hanasu fadar gaskiya, wasu kuma kwadayi ke hanasu bin Allah. Saboda haka mafita dayace mu aje fadan akidu da mazhabobi mu rungumi alkurani muyi masa gata, mu tsayu kyam akan “BABU HUKUMA SAITA ALLAH”(Lailaha illallah) Wannan kadaine zai fitar damu daga kangin kunci da talauci da jahilci wanda wadannan azzaluman mahukunta karnukan yahudawa suka sakamu a ciki, da taimakon Allah zamuyi nasara. Amma me kake tunanin zamu gayawa Allah(t) ranar kiyama idan ya tambayemu wane kokari mukayi na dawowa da dokokinsa(Alqurani) yayinda aka bijere daga binsa akabi wasu dokoki (dokokin turawan mulkin mallaka) sabanin nasa? Kaga bamu fara cemasa sako baizoba. Saboda haka kuci gabada yada irin wannan daawa tanada matukar mahimmanci wajen ciyarda addini gaba, da fatan Allah(t) ya karfafamu. Walhamdu lillahi rabbil alamin.

Leave a Reply to Ahmad Yusuf AssqalainiCancel reply

Latest updates
Categories