KWANAKIN HAJJI (RANA TA BIYU)(Mal.Aminu Ibrahim Daurawa)

Rana ta biyu itace ranar Arfa,
Manzon Allah saw yace, Babu
wata rana da Allah yake yanta bayi
daga wuta, kamar ranar Arfa,
Muslum
A wani Hadisin yace: Mafi alkhairin
Addu’a itace Addu’ar ranar Arfa,
Attirmiziy,
Azumin ranar Arfa, yana kankare
zunubin shekarar data gabata, da
mai zuwa, Muslum, ( wannan ya
shafi, wadanada basu zo hajji ba )
abubuwan da akeyi ranar Arfa
1- Tasowa daga mina zuwa filin
Arfa
2- Gabatar da Hudubah, ga duk
musulmin duniya akan Tauhidi, da
hadin kai, da tattauna matsalolin
Musulmi
3- Yin Sallar Azahar da Laasar,
Kasaru da Jam’i, a lokacin Azahar
4- Shagala da addua, da zikiri, da
salati, yiwa Allah kirari, da
siffofinsa da sunayansa,
5- Har zuwa faduwar Rana, kafin
shirin tafiya zuwa filin Muzdalifah,
domin gabatar da Sallar magariba
da Ishah, a kwana zuwa ranar
goma ga wata.
Muyi addua ta gari, Allah ya
daukaka musulunci da musulmi

Leave a Reply

Latest updates
Categories
%d bloggers like this: