HUKUNCE-HUKUNCEN AIKIN HAJJI DA UMRA Darasi na 11(Sheikh Abdulwahhab Abdullah)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

SIFFAR HAJJI A RARRABE:
RANAR 8 GA WATA
-Alhajin da yake akin hajji na
Kirani ko Ifradi, kasancewar suna
cikin ihiraminsu, sai su tafi Mina.
Shi kuwa mai tamattu‘i wanda ya
cire ihiraminsa tun bayan ya
kammala aikin Umra, a wannan
rana ta 8 ga wata, sai ya yanke
farce, ya aske duk wani gashi
wanda bukatar aske shi ka iya
tasowa.
-Sai yayi wanka ya sanya
ihiraminsa daga inda yake a
Makka.
-Idan ya kasance Alhaji ya haure
mikati, don zuwa ziyara ko wani
al’amari, anso masa ya sake
shigowa Makka yana me umra.
-Idan lokacin daukar haramarsa
lokacin sallah ne, ta farilla ko ta
nafila, anso yayi sallah sannan
yayi harama yace:
ﻟﺒﻴﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﺣﺠﺎ
idan kuma ba lokacin sallah ba ne,
ba sai yayi wata sallah ba.
-Alhaji zai yawaita talbiyyah akan
hanyarsa ta zuwa Mina, kuma
anso sallar azahar ta riske shi
acan.
-Zai yi sallolin azahar da la‘asar,
kowaccensu kasaru kuma akan
lokacinta.
-Alhaji ya kula da yawan karatun
Kur‘ani da yin talbiyyah da istigfari
da hailala da salatin Annabi
sallallahu alaihi wa sallama.
RANAR 9 GA WATA:
-Idan ya wayi gari ranar 9 ga wata,
wato ranar arafa, sai ya tafi filin
Arfa. Anso ya isa kafin azahar, sai
ya bi liman ya sallaci azahar da
la‘asar kowacce kasaru, ana idar
da wannan a tayar da dayan.
Wanda kuwa bai sami zuwa da
wuri ba sai ya hadu da ire-irensa
su yi jam‘i a cikin shema.
-Wadanda shemar su take wajen
filin arfa wajibi ne suyi kokari su
shiga da‘irar filin arafa koda bayan
faduwar rana ne domin babu hajji
ga wanda bai tsaya a Arafa ba.
-Alhajin da ya sami shiga arafa da
abin hawansa, anso ya fuskanci
alkibla yana akansa, idan bai samu
ba ya tsaya a tsaye, idan ba zai iya
ba sai ya zauna, ya daga hannu ya
yita addu‘a har faduwar rana ko
kuma idan ya gaji sai ya huta.
-Alhaji ba zai bar Arafa ba har sai
rana ta fadi, kuma ba zai yi sallar
magrib ba har sai ya isa Muzdalifa.
-zai yi sallar magriba da isha‘i a
lokaci daya a Muzdalifa, kuma
babu sallar nafila a tsakanin su.
-Alhaji zai kwana a Muzdalifa
sannan ya isa Mash‘arul Haram
bayan sallar asuba, sai ya tsaya a
tsaye yana fuskantar Alkibla, yana
yawaita hamdala da hailala da
salati da tasbihi d.s.
Wadannan su ne aiyukan ranakun
8 da na 9 ga wata.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories