HUKUNCE-HUKUNCEN AIKIN HAJJI DA UMRA Darasi na 12(Sheikh Abdulwahhab Abdullah)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

RANAR 10 GA WATA
Idan Alhaji ya kwana a Muzdalifa
ranar Arafa ya wayi gari ranar 10
ga wata, idan yayi sallar asuba sai
ya isa Mash‘arul Haram
(masallacin Muzdalifa), idan bai
samu guri a da’irarsa ba zai tsaya
a duk inda ya samu a Muzdalifa,
sai ya fuskanci Alkibla ya yawaita
addu‘oi da zikiri da salati da
kabarbari.
-Idan gari yayi haske sosai kafin
fitowar rana sai ya tafi Mina. Yana
iya tsintar tsakonkonin yin jifa guda
7 a kan hanyarsa, (girmansu
gwargwadon gabar dan yatsan
hannu,) amma ba zai wanke su ba
domin wanke su bidi‘a ne.
-Idan ya isa Mina zai jefi Jamratul
Akaba da wadannan tsakonkonin.
-Daga nan sai yayi yanka.
-Bayan nan sai yayi aski ko yayi
saisaye, amma yin askin yafi. Su
kuwa mata sai su aske karshen
gashinsu, gwargwadon gabar
yatsa.
-Daga nan yana iya sanya kayan
gida, sai ya tafi Makka yayi
Dawaful Ifadah (amma ba zai yi
sassarfa a zagaye ukun farko
kamar yadda yayi a baya ba).
– Idan Tamattu’I yake yi sai ya je
yayi sa‘ayi tsakanin Safa da
Marwa. Su kuwa masu yin Ifradi ko
Kirani indai sun riga sunyi sa‘ayi na
farko ba sai sun maimaita ba.
-Idan ya yi sa’ayin sai ya tafi Mina
don yin kwanakin Mina kwana 2 ko
3 wadanda karin bayani zai zo a
kansu insha Allahu.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories