ME YA FARU A KARBALA 31(Dr. Mansur Sokoto)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Matsayin Malaman Sunna A Kan
Wadannan Fitinu
Annabinmu Sallallahu Alaihi Wa
Alihi Wasallam ya sanar da cewa
fitinu zasu gudana a bayansa.
Kuma ya fadi cewa alherinka yana
gwargwadon nisantarka daga gare
su. Wadannan hadisai suna nan a
shimfide cikin littafan Sunna a
Kitabul Fitan na kowane littafi.
Duba alal misali: Sahihul Bukhari,
Kitabul Fitan, Babun takunu
fitnatun al qa’idu fi ha khairun minal
qa’im, Hadisi na 6670.
Game da abinda ya faru a Karbala,
ba wani sabani a tsakanin malamai
cewa, an tafka barna wadda ba ta
dace ba. Abin takaici ne da ya
nuna cewa ba a mutunta Manzon
Allah Sallallahu Alaihi Wasallam
ba a cikin sha’anin iyalinsa. Wanda
kuwa duk yake da hannu a ciki to,
ba abinda zai hana shi gamuwa da
fushin Allah in ba tuba ya yi ba
tuba ingatacciya.
Amma a game da wa ke da alhakin
wannan ta’asa, to kowa ya fadi
albarkacin bakinsa. Duk wanda
yake da kyakkyawan nazari da sa
adalci cikin hukunci zai iya lura da
cewa kaddarar Allah ita ce babban
jigon abinda ya faru. Kuma duk
abinda ka ga Allah ya yi to, tabbas
akwai hikima a cikinsa, ko mun san
ta ko bamu sani ba. Hasashen da
Ibnu Taimiyyah ya yi a nan abin
sauraro ne matuka. Ga abinda ya
ce:
Hasan da Husaini sun rayu a cikin
kuruciya zamanin Manzon Allah
Sallallahu Alaihi Wa Alihi
Wasallam. Don haka ba su samu
damar taimaka masa ba a wajen
jihadi da yada kalmar Allah kamar
yadda sauran sahabbai suka yi.
(Misali, ko da aka fara yakin Badar
da na Uhud ko auren Nana Fatima
da angonta sayyidina Ali (R.A) ba a
daura ba). Duk wahalhalun da
sahabbai suka sha a Makka da
tsangwama da tashin hankali, haka
ma duk gwagwarmayar da suka yi
bayan sun bar gidajensu da
yakokan duk da aka yi; Badar da
Uhud da Khandak da Tabuk da
sauransu inda Allah ya yi ta rabon
darajoji da gafara ga sahabbai
(kamar yadda zamu gani a Suratu
Ali Imran da Taubah da Ahzab da
Fathi dss) su wadannan bayin
Allah ba su samu kasancewa a ciki
ba. Kasancewar Allah ya zaba
masu wani babban matsayi a
aljanna ya sa dole ne su ma su
fuskanci wasu kalubale da zasu kai
ga samun shahadarsu domin
daukakar matsayinsu. Don haka
ma Ibnu Taimiyyah ya kara da
cewa, kashedinka ka zargi Husaini
a kan fitowar da ya yi bayan duk
shawarwarin da aka ba shi. Ka
sani Allah ne yake ingiza shi zuwa
ga daukaka da darajar da ya
hukunta masa. Duba Minhajus
Sunnatin Nabawiyyah na Ibnu
Taimiyyah (4/527-536).

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories