ME YA FARU A KARBALA 2(Dr. Mansur Sokoto)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Assalamu alaikum jama’a.
Ina kara jaddada barka da sallah a
gare ku gaba daya. Allah ya karbi
ibadarmu.
Zamu ci gaba da darasi na biyu a
yau in sha Allah.
Tun da farko zai yi kyau mu soma
da takaitaccen tarihin mutane biyu
wadanda zancen Karbala yake
kewaya a kan su. Su ne: Sayyidina
HUSAINI bin Ali da kuma YAZIDU
dan Sayyidina Mu’awiyah.
Wane ne HUSAINI?
Shi ne jikan Manzon Allah
Sallallahu Alaihi Wasallam
HUSAINI Dan Ali Dan Abu Dalib
Dan Abdulmuttalibi Dan Hashimu
Al Hashimi. Mahaifiyarsa ita ce
Fatimah Diyar Manzon Allah
Sallallahu Alaihi Wasallam.
An haife shi a cikin watan
Sha’aban na shekara ta hudu
bayan hijira.
(watanni 11 ke tsakanin sa da
wansa Al Hasan).
Manzon Allah Sallallahu Alaihi
Wasallam ne ya sanya masa suna,
ya kuma yanka masa rago.
A Lokacin wafatin Manzon Allah
Sallalahu Alaihi Wasallam
HUSAINI na da shekara 6 da wata
7.
HUSAINI ya fi kowa kama da
Manzon Allah Sallallahu Alaihi
Wasallam ta kasan jikinsa. Amma
Al Hasan ya fi shi kama da shi ta
saman jiki.
Sun tashi kamar tagwaye saboda
kusancin shekarunsu kuma
Manzon Allah Sallallahu Alaihi
Wasallam ya kasance yana son su
da kaunar su irin so da kaunar da
ba sa boyuwa. Ya kan kuma yi
musu addua yana cewa, “Ya Allah!
Hakika ina son su, Ya Allah kai ma
ka so su”.
Wannan ya sa masu kwarjini da
kauna ba na wasa ba a wurin
Sahabbai wadanda kaunar da
suke ma Manzon Allah Sallallahu
Alaihi Wasallam ta sa suna son
duk abinda yake so kuma yake
kauna.
HUSAINI ya yi tarayya da Dan
uwansa Al Hasan a wata falala
wadda suka kebanta da ita, ita ce
kasancewar su shugabannin
matasan aljanna.
(Al Jami’ na Tirmidhi, Hadisi na
3768 da Al Musnad na Ahmad (3/3
da 3/62) da Al Mustadrak na Hakim
(3/167). Kuma Tirmidhi ya inganta
shi.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories