SAHIHIYAR AQIDA ITA CE JIGO CIKIN ADDINI:(Sheikh Aliyu Said Gamawa)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Allah mai girma da daukaka ya aiko
dukkan Manzanni don isar da sakon
sa ga bayinsa zamani bayan zamani,
kuma dukkan su farkon kiransu yana
farawa ne kan TAUHIDI, wato a
kadaita Allah shi kadai cikin halitta da
sunaye da bauta.
Hakika dacewa da samun sahihiyar
aqida babbar ni’imace, kuma baiwace
mai girma. zama cikin kazamtar shirka
da kafirci sune tabewa da halaka
duniya da lahira.
‘Yan uwa na maza da mata lallai mu
nisanci bin dukkan hanyoyin da zasu
kaimu ga rushewar imani, da barin
sahihiyar hanya ta Tauhidi.
Mu nisanci hada Allah da wani cikin
bauta ta hanyar bautar gumaka, ko
kiransa da sunayen da ba nasa ba, ko
yi masa shirka cikin abinda ya halitta,
ko kafircewa ta hanyar cewa Allah
yana da ‘da, ko imani da wani
kulumboto, ko rantsuwa da wani
baicin Allah, da kiran wani ba Allah ba
cikin makabartu, ko yayin addu’a, ko
ambaton wanin Allah in za’a yi yanka,
da halaka ta hanyar fadawa layin
sihiri, bokanci da sauran aiyukan
shirka iri iri na neman taimako, ko
agaji daga wanin Allah, ko rokon ruwa
ko arziki ko haifuwa daga wani ba
Allah ba.
Mu ji tsoron Allah ya bayin Allah, mu
sani Allah yana yafe dukkan zunubbai
amma banda shirka, kuma har Annabi
(saw) ance masa.. in da za kai shirka,
da sai mu bata aiyukan ka… Tsarki ya
tabbata ga Allah wanda yayi halitta
shi kadai, kuma shi ake bautawa shi
kadai ta da ya aiko Annabin mu
Muhammad (saw), kuma gareshi
muka dogara, kuma gareshi muke
rokon komi da neman kowanni agaji
da taimako. Hakika sunayen sa
madaukaka ne, masu kyau da tsaki
kuma lahani baya shiga cikin su daga
muminin bawa.
Allah muke roko ya yi dadin tsira da
aminci ga annabi (saw).

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories