WANENE MAI DA”AWAH ???(Sheikh Muhammad Kabir Haruna Gombe)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Da yawan Mutane na zaton cewa; Kira zuwa ga Musulunci da Nusar da Musulmai kan Turbar Annabi, aiki ne da ya takaita ko ya rataya kan Manyan Malamai da Kuma Ustazai da wadanda ke da Ruwa da Tsaki cikin harkar Addini.
Aikin fadada Musulunci da Gyarawa Mutane zama a cikinsa, Nauyi ne da ya rataya kan Wuyan kowane Musulmi da Musulma, Manzon Allah yace:
“ Ku isar da Sako daga gareni, ko da Aya Daya ce kawai kuka sani”
Sau da yawa in Manzon Allah ya kammala zance sai yace:
“Wanda ya zo ya sanarwa Wadanda ba su sami damar zuwa ba”
Ashe, Duk wanda ya san Aya Daya, Nauyin kira zuwa ga Allah ya hau kansa inji Bakin da baya Karya(s.a.w).
Samari !! da Dattawa!! Ya zama muku Tilas ku tambayi kanku ?? Wace Gudummawa kuka bayar na Habaka wannan Tafiya?? A cikin Gidajenku ko tsakanin Abokanku?? Wajen Aikinku ko Kasuwancinku??
Allah zai tambayeka kan Damar da ka samu amma ba ka yi amfani da ita ba!!
Shin In wani zance ko Nasiha ta shige ka, Ka taba Sharing da Abokanka ??
Wa yace maka sai ka haddace Ayoyi da yawa?? Ko sai ka Iya Larabci?? Ko sai an nadaka liman?? Abinda ba a so shine; Ka fadi abinda baka da Masaniya a kansa?? Wannan kam in ka aikata zaka sha Azaba Ran Qiyama. Annabi(s.a.w.)yace:
“ Wanda ya yi min Karya da gangan ya tanadi Matsuguninsa a Wuta ranar Qiyamah”
Allah yasa Mu Dace.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

5 responses to “WANENE MAI DA”AWAH ???(Sheikh Muhammad Kabir Haruna Gombe)”
  1. Aliyu said gamawa Avatar
    Aliyu said gamawa

    Jazakallahu khairan

  2. ANAS A.ALIYU Avatar
    ANAS A.ALIYU

    ALLAH YA TSAREMU

  3. Maimuna Avatar
    Maimuna

    Allah ya sakawa malam da alheri ya tsareshi sharrin makiya.

  4. uairu ismail Avatar

    allah ya karo ilimi malan

  5. Yusif Usman Yusif Avatar
    Yusif Usman Yusif

    Allah Ya Karemu, Ya Kare Addininmu,

Leave a Reply

Latest updates
Categories