Addu’ar haduwa da abokin gaba ko wanda ake jin tsoron sa

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Abu Musa Al-Ash’ary Allah ya ƙara masa yarda yace:

Annabi Tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance idan yaji tsoron wasu mutane sai yace “Allahumma inna naj’aluka fi nuhurihim, wa na uzu bika min shururihim”. اللهم إنا نجعلك في نحورهم ونعوذ بك من شرورهم

Abu dawud: 1537,. Annasa’i: 8631,. Ahmad: 19720

Fassarar Addu’ar

Ya Allah muna sanya ka a mayankan su Ma’ana ( ka tsare mu daga sharrin su idan suka nufe mu da mummunan abu) sannan muna neman tsarinka da sharrukan su.

Wannan addu’a ana yinsa ne idan mutum zai haɗu da wanda yake jin tsoron sa, ko abokin gaban sa da yake jin tsoron zai cutar dashi.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories