Fatawowin Rahama By Dr. Sani Umar Rijiyar Lemu 24-11-2019

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Fatawa

Tambayoyi da amsoshin dake ciki


  1. Hukuncin wanda ya taya ‘yar uwanshi duren kunu ma danta marar lafiya. Sannan bayan dura mishi kunu sai yaron ya rasu. (Daga minti 2 zuwa minti 3)
  2. Hukuncin qarasa fadin Muhammadu rasulluh a qarshen iqama, la’akari da hadisin da yake cewa marowaci shine wanda aka kiran sunan Annabi bai masa salati ba (Daga minti 3 zuwa minti 8)
  3. Qarin bayan akan ayar – واعبد ربك حتى يأتيك اليقين (Daga minti 8 zuwa minti 10)
  4. Hukuncin wanda yake bin bashi, ya zame kudin da yake bi bashi lokacin zakka (Daga minti 10 zuwa minti 11).
  5. Hukuncin cin naman dake amfani da qwayoyin hallita samar da naman shanu da raguna “laboratory meat” (Daga minti 11:57 zuwa minti 13)
  6. Mace mai takaba zata iya fita bayan kwana arbain? (Daga minti 13 zuwa minti 15)
  7. Musulmi zai iya amfana da kudin mahaifinshi wanda ba musulmi ta hanyar wassici? (Daga minti 15 zuwa minti 16)
  8. Hukuncin mijin da ya mari matar shi saboda sa’in-sa da ya shiga tsakaninsu (Daga minti 16 zuwa minti 17)
  9. Adadin da yazo na karanta ayatul qursiy da suratul Ikhalas, da Muawidhatain a lokacin adhkar din safiya (Cikin minti 17).
  10. Bayyana rashin cin karo tsakanin ayar da take cewa babu tilas a addini da kuma hukuncin haddin kisa da ake yi ma wanda yayi ridda (Daga minti 17 zuwa minti 22)
  11. Ya hallata mutum da yake sayan kayan gona ma wani, ya sanya ladan shi akai? (Daga minti 22 zuwa minti 23)
  12. Ya hallata mutum ya ware wata rana domin bada sadaka? (Daga minti 23 zuwa minti 24)
  13. Ya hallata mutum yace “ta ya Allah kiwo yafi Allah na nan” (Daga minti 24 zuwa minti 26)
  14. Hukuncin wanda ya manta tahiya a sallah (Cikin minti 26 )
  15. Banbacin hukunce -Hukunce tsakanin azumin farilla da azumin nafila (Daga minti 26 zuwa minti 29)
  16. Lokacin karbar addua- shine tsakanin kiran sallah da iqama ko iqama da kabbarar harama (cikin minti 29).
  17. Akwai laifi ga dan kasuwan da yake sayar da kayan da mutanen china suke masa a Nigeria ma ‘yan Nigeria batare da ya bayyana musu a Nigeria ake yi kayan godon kada su ki sayan kayan? (Daga minti 29 zuwa minti 31)
  18. Akwai ingantacce hadisi akan matsar qabari? (Daga minti 32 zuwa minti 33)
  19. Hukuncin wanda ya manta karatun Sura a cikin sallah (cikin minti 33)
  20. Menene gaskiyan ba a zagin Shaidan (Cikin minti 34)
  21. Menene sahihancin cewa baitul ma’amur yana daidai da saitin ka’aba. (Daga minti 34 zuwa minti 35)
  22. Shin hidimar mace ga mijinta wajibi ne (Daga minti 35 zuwa minti minti 38)
  23. Mai karanta littafin “Qawa’idi” ma wanda basu sani ba- yana karantar da su abinda ya sani ba dadi ba qari yana da laifi? (Cikin minti 38)
  24. Fassarar hadisin “ wanda ya ambaci Allah shi kadai, ya zub da hawaye” (Cikin minti 39)
  25. Shin hadisin “…kullu bidiatin dalala na Irbad bin Sariya (Radiyallahu anhu)bai inganta ba? (Daga minti 40 zuwa qarshe)

Download

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

One response to “Fatawowin Rahama By Dr. Sani Umar Rijiyar Lemu 24-11-2019”
  1. […] Archive Fatawowin Rahama 24-11-2019 Fatawowin Rahama 23-11-2019 Fatawowin Rahama 16-11-2019 Fatawowin Rahama 02-11-2019 […]

Leave a Reply

Latest updates
Categories