Hukuncin shan ruwa a tsaye

Danna nan domin shiga Online Islamiyya.

Ana koyar da Hada baki, da Qur’ani da sauran su

Anas bin Malik ya rawito Annabi Sallallahu alaihi Wasallama yayi tsawa game da shan abu a tsaye kamar yadda Muslim ya rawaito a hadisi 2024.

Wannan hadisi ne a bayyane da yake nuni kan hanin Mutum yasha abu a tsaye. Sai dai kuma an sake rawaito wani hadisin daga ibn Abbas cewa Annabi Sallallahu alaihi Wasallama yasha ruwan Zam Zam a tsaye. Kamar yadda Muslim ya rawaito a hadisi mai lamba ta 5617.

Haka nan An rawaito daga Aliyu Bin Abi ɗalib an kawo masa ruwa yasha a tsaye sai yace:

Wasu mutane suna ƙin shan ruwa a tsaye, toh haƙiƙa naga Annabi ya aikata kamar yadda nima na aikata.

Sahihul Bukhari Hadith No: 5615

Wannan hadisai biyu da muka kawo a ƙarshe suke nuna halaccin shan ruwa a tsaye.

Imamun-Nawawy da Ibnul Qayyim sun Rajjaha cewa shan abin sha a tsaye Makruhi ne amma ba mai ƙarfi ba, Sabida haka ne ma Annabi yasha a tsaye sabida ya nuna halaccin sa in akwai buƙatar hakan.

Sabida haka: Shan ruwa a tsaye Ba haramun bane sai dai sha a zaune shine yafi dace wa kuma mutum yafi samun natsuwa, amma in mutum yasha a tsaye sabida buƙata toh babu laifi a hakan.

Allah yasa mudace.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Categories
Latest updates