ME YA FARU A KARBALA 7(Dr. Mansur Sokoto)

·

·

Domin neman ƙarin bayani danna nan

Kafin mu karkare magana kan
Yazidu yana da kyau a san
abubuwan da Ahlussunna ke
la’akari da su wajen yanke hukunci
a kan kowane mutum.
1. Musulmi duk yana da alfarmar
da ya kamata a kiyaye masa. Ba
ya halasta a shiga rigar
mutuncinsa sai da dalili
tabbatacce.
2. Kuskure a wajen kyautata ma
musulmi zato ya fi alheri bisa yin
daidai wajen cin zarafinsa. Domin
a na farkon, Allah na iya yi ma
uzuri, amma a na biyun mai alhaki
zai ja alhakinsa a gaban Allah.
3. Wanda bai gani da idonsa ba, ko
ya ji da kunnensa, to idan ya ba da
sheda, shedarsa ba kammalalliya
ba ce, domin ba ta ginu a kan ilmi
ba. Kamar yadda Allah ya ce:
(( ﺍﻻ ﻣﻦ ﺷﻬﺪ ﺑﺎﻟﺤﻖ ﻭﻫﻢ ﻳﻌﻠﻤﻮﻥ(( ﺳﻮﺭﺓ
ﺍﻟﺰﺧﺮﻑ: ٨٦
“Sai dai wadanda suka yi shaida
da gaskiya, kuma suna sane (da
abin da suka yi sheda a kansa).
4. Maganar abokin gaba ba a
karas da ita sai an tabbatar da
tsarkin zuciyarsa da gaskiyar
harshensa. Amma abokin gaba da
aka san shi da shara ta to sai anyi
nazari an duba sauran ruwayoyi
sannan a yanke hukunci a kan
riwayarsa.
5. A kan kowane mutum akwai
abinda yake yuwa a jingina masa.
Ko a cikin abokanenka da zaran an
ce wane ya yi kaza, zaka yi fararat
ka ce a’a. Ba dai wane ba. Wani
kuma da zaran an fada zaka ce
karamin aikinsa ne. Wannan fa tun
baka bincika ba kenan, to ina ga ka
tambaye shi ya karyata zargi?
Wannan shi ya sa yake da kyau
mu san cikakken tarihin mutum
kafin mu dau matsayi a kan duk
wani labari da aka jingina masa.
Kuma wannan shi ya sa masu
hankali ke taka birki in an zo
magana kan almajiran Annabi
Sallallahu Alaihi Wa Alihi
Wasallam la’akari da dinbin yabon
su da muke ta karantawa kullum a
cikin maganar Allah. Wanda Allah
ya saukar da dawwamammen littafi
ana karantawa a kan yabon sa, zai
yiwu ya zama shi ne abin zargi?
6. Mutum ya kan iya yin laifi kome
girmansa amma ya kasance ya
tuba daga bisani ko ya gamu da
wani hukuncin Allah a nan duniya
wanda zai shafe laifinsa, ko
ladarsa ta rinjayi zunubinsa, ko ya
samu gamon katar da ceton
Manzon Allah Sallallahu Alaihi
Wasallam ko Allah ya dubi tsarkin
zuciyarsa ya yafe kurensa ko ya
yafe masa laifinsa. Don haka ya sa
Ahlussunna ba su zagi, ba su
la’anta domin ba su son shiga
tsakanin mutum da mahaliccinsa.
Wadannan ka’idoji ne da suka
shafi kowa da kowa. Ba ina nufin
Yazidu ba. Amma maganar
Yazidun da nasa laifi tana nan tafe.

One response to “ME YA FARU A KARBALA 7(Dr. Mansur Sokoto)”
  1. Kabir bawa kulere Avatar
    Kabir bawa kulere

    Jazakallahu bikhair.

Leave a Reply

Latest updates
Categories