Tahiyyatul Masjid(Gaisuwar Masallaci)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Menene Tahiyyatul Masjid? Kuma meye Hukuncin ta?

Tahiyyatul Masjid itace raka’oi biyu da Mutum zaiyi da zarar ya Shiga Masallaci kafin ya zauna.

Hukuncin ta: Sunnah ce

Dalili: an rawaito daga Abu Qatada Allah ya ƙara masa yarda yace:

Annabi Tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi yace: idan ɗaya daga cikin ku ya shiga Masallaci kada ya zauna har sai yayi Sallah raka’a biyu

Bukhari: 930. Muslim: 875

Haka nan an sake rawaito wa Jabir Allah ya ƙara masa yarda yace

Sulaik Algaɗfani ya shigo masallaci Annabi Tsira da Amincin Allah su tabbata a gare shi yana huɗuba sai ya zauna sai Annabi yace masa ka tashi kayi raka’a biyu amma ka taƙaita.

Bukhari: 930. Muslim: 875

Wannan yake nuna a kowani lokaci mutum ya shiga Masallaci zaiyi wannan raka’a guda biyu koda ranar Juma’a ne Limami yana huɗuba.

Sannan Tahiyyatul Masjid tana faɗuwa idan mutum ya shigo masallaci ya samu ana sallah, ko ana gab da a fara sallah kuma lokaci bazai bashi dama yayi rakao’in biyu ba.

Tahiyyatul Masjid a Masallaci mai alfarma:

Idan mutum yaje Ka’aba da nufin yin ɗawafi to wannan ɗawafin ya maye gurbin Tahiyyatul Masjid, amma idan yaje domin sallah ne ko karatu ko wani abu to hukuncin sa ɗaya da sauran masallatai zaiyi wa’innan raka’oi guda biyu

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories