Mas'alolin aure Fitowa ta 12(Sheikh Abdulwahhab Abdullah)

ยท

ยท

Bayani game da dalilan da Shiโ€™a Imamiyya suke kafa hujja da su don halatta auren mutu’a:
1-
(A)- Da farko dai ayar da suka dogara da ita ko kadan ba dalili ba ce a kan halaccin auren mutuโ€™a; domin kuwa tana magana ne a kan ingantaccen aure na dindindin, da kuma abin da ya wajaba a baiwa mace na sadakinta. Abinda yake nuna wannan maganar shine; farkon ayar Ubangiji subhanahu wa ta’ala yana magana ne akan matan da bai halatta a aura ba, sannan sai ya yi magana akan yin aure wanda yake sananne a shariโ€™a. Ya ce:
ูˆูŽุงู„ู’ู…ูุญู’ุตูŽู†ูŽุงุชู ู…ูู†ูŽ ุงู„ู†ู‘ูุณูŽุงุกู ุฅูู„ู‘ูŽุง ู…ูŽุง ู…ูŽู„ูŽูƒูŽุชู’ ุฃูŽูŠู’ู…ูŽุงู†ููƒูู…ู’ ูƒูุชูŽุงุจูŽ ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ุนูŽู„ูŽูŠู’ูƒูู…ู’ ูˆูŽุฃูุญูู„ู‘ูŽ ู„ูŽูƒูู…ู’ ู…ูŽุง ูˆูŽุฑูŽุงุกูŽ ุฐูŽู„ููƒูู…ู’ ุฃูŽู†ู’ ุชูŽุจู’ุชูŽุบููˆุง ุจูุฃูŽู…ู’ูˆูŽุงู„ููƒูู…ู’ู…ูุญู’ุตูู†ููŠู†ูŽ ุบูŽูŠู’ุฑูŽ ู…ูุณูŽุงููุญููŠู†ูŽ ููŽู…ูŽุง ุงุณู’ุชูŽู…ู’ุชูŽุนู’ุชูู…ู’ุจูู‡ู ู…ูู†ู’ู‡ูู†ู‘ูŽ ููŽุขุชููˆู‡ูู†ู‘ูŽ ุฃูุฌููˆุฑูŽู‡ูู†ู‘ูŽ ููŽุฑููŠุถูŽุฉู‹โ€ฆ ุงู„ู†ุณุงุก2
Maโ€™ana:
Haka kuma an haramta muku (auren) katangaggun mata (wato matan da suke karkashin aure), face abinda kuka mallaka na kuyangi, (wannan) hukuncin Allah ne a gare ku tabbatacce. Kuma an halatta muku koma bayan wadannan(nau’ikan matan da aka ambata), ku aure su da dukiyoyinku, kuna masu kare kanku, ba masu zina ba. Abin da kuka ji dadi da shi daga gare su (na saduwar aure), to, ku ba su ladansu na sadakiโ€ฆ
Ambaton kalmar” ujurahunna” โ€œladan suโ€ ba yana nufin ladan mutuโ€™a ba ne , domin Allah yakan ambaci “sadakin aure” da kalmar”ujuur” (ladan aure) kamar yadda ya ke a wurare da dama a cikin Al-Kurโ€™ani Mai Girma, misali :
ูŠูŽุง ุฃูŽูŠู‘ูู‡ูŽุง ุงู„ู†ู‘ูŽุจููŠู‘ู ุฅูู†ู‘ูŽุง ุฃูŽุญู’ู„ูŽู„ู’ู†ูŽุง ู„ูŽูƒูŽ ุฃูŽุฒู’ูˆูŽุงุฌูŽูƒูŽ ุงู„ู„ู‘ูŽุงุชููŠ ุขุชูŽูŠู’ุชูŽ ุฃูุฌููˆุฑูŽู‡ูู†ู‘ูŽโ€ฆ ุงู„ุฃุญุฒุงุจ: 50
Maโ€™ana:
Ya kai Annabi (mai girma)! Hakika Mu, mun halatta maka matanka wadanda ka baiwa “ujuur din su” (sadakin aurensu)โ€ฆ
Kalmar ujurahunna a nan babu ko shakka sadakin aure take nufi, ba wai ladan mutuโ€™a ba.
Da kuma fadinsa:
ููŽุงู†ู’ูƒูุญููˆู‡ูู†ู‘ูŽุจูุฅูุฐู’ู†ู ุฃูŽู‡ู’ู„ูู‡ูู†ู‘ูŽ ูˆูŽุขุชููˆู‡ูู†ู‘ูŽ ุฃูุฌููˆุฑูŽู‡ูู†ู‘ูŽ ุจูุงู„ู’ู…ูŽุนู’ุฑููˆููโ€ฆยญุงู„ู†ุณุงุก: 25
Maโ€™ana:
Ku aure su bisa izinin waliyyansu, kuma ku ba su”ujuur din su” (sadakinsu) bisa kyautatawaโ€ฆ
A nan ma kalmar โ€œujurahunnaโ€ sadaki ake nufi ba ladan mutuโ€™a ba.
(B)- Ita kuwa hujjar da suka kafa na kiraโ€™ar da ake cewa kira’ar Ubayyu Ibn Kaโ€™ab da Abdullahi Ibn Abbas ุฑุถูŠ ุงู„ู„ู‡ ุนู†ู‡ู…ุง kiraโ€™a ce shazza, wadda malaman kiraโ€™a ba sa kirga ta a cikin tabbatattun kiraโ€™oโ€™i. Ita kuwa Kiraโ€™a Shazza ba za ta ci karo da tabbatacciyar kiraโ€™a mutawatira ba, inda Ubangiji subhanahu wa ta’ala ya fada a Suratul Muminun:
ูˆูŽุงู„ู‘ูŽุฐููŠู†ูŽ ู‡ูู…ู’ ู„ูููุฑููˆุฌูู‡ูู…ู’ ุญูŽุงููุธููˆู†ูŽ (5) ุฅูู„ู‘ูŽุง ุนูŽู„ูŽู‰ ุฃูŽุฒู’ูˆูŽุงุฌูู‡ูู…ู’ ุฃูŽูˆู’ ู…ูŽุง ู…ูŽู„ูŽูƒูŽุชู’ ุฃูŽูŠู’ู…ูŽุงู†ูู‡ูู…ู’ ููŽุฅูู†ู‘ูŽู‡ูู…ู’ ุบูŽูŠู’ุฑู ู…ูŽู„ููˆู…ููŠู†ูŽ (6) ููŽู…ูŽู†ู ุงุจู’ุชูŽุบูŽู‰ ูˆูŽุฑูŽุงุกูŽ ุฐูŽู„ููƒูŽ ููŽุฃููˆู„ูŽุฆููƒูŽ ู‡ูู…ู ุงู„ู’ุนูŽุงุฏููˆู†ูŽ (7)ุงู„ู…ุคู…ู†ูˆู†:7โ€“ 5
Maโ€™ana:
(Hakika Muminai) Su ne masu kiyaye farjinsu. Saifa ga matayensu, ko abin da suka mallaka na kuyangi, hakika wadannan ba abin zargi ba ne. Wanda duk ya nemi (wani abu) koma bayan wannan, wadannan su ne masu shisshigi da ketare dokokin Allah.
Abin fahimta a nan shine Allah ya bayyana cewa mace ba ta halatta ga mutum, sai ta wadannan hanyoyi guda biyu, ko dai aure na dindindin ko kuma mallakar kuyanga, amma bai yi maganar auren mutuโ€™a ba. Sannan a karshen ayoyin, Allah ya yi bayanin narko ga wanda ya nemi jin dadi da wata mace sabanin ta hanyar da aka ambata.
(C)-Kuma idan ma muka dauka cewa waccan kiraโ€™ar tabbatacciya ce, to, duk da haka ba za ta zama hujjar yin auren mutuโ€™a ba, saboda kaโ€™idar da malaman Usulu suke cewa; โ€œIdan dalilan halattawa da na haramtawa suka hadu akan masโ€™ala daya, to, ana gabatar da dalilin haramtawa.
2-
(A)- Hujjar su ta biyu; game da fatawar Abdullahi Ibn Abbas radhiyallahu anhuma na halatta auren mutuโ€™a, wannan ya faru ne a farkon lamari, amma daga baya an sanar da shi haramta auren mutuโ€™a da Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama yayi har zuwa ranar alkiyama.
Imamu Muslim ya rawaito hadisi cewa:
ุนูŽู†ู’ ุนูŽู„ูู‰ู‘ู ุฃูŽู†ู‘ูŽู‡ู ุณูŽู…ูุนูŽ ุงุจู’ู†ูŽ ุนูŽุจู‘ูŽุงุณู ูŠูู„ูŽูŠู‘ูู†ู ููู‰ ู…ูุชู’ุนูŽุฉู ุงู„ู†ู‘ูุณูŽุงุกู ููŽู‚ูŽุงู„ูŽ ู…ูŽู‡ู’ู„ุงู‹ ูŠูŽุง ุงุจู’ู†ูŽ ุนูŽุจู‘ูŽุงุณู ููŽุฅูู†ู‘ูŽ ุฑูŽุณููˆู„ูŽ ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ู†ูŽู‡ูŽู‰ ุนูŽู†ู’ู‡ูŽุง ูŠูŽูˆู’ู…ูŽ ุฎูŽูŠู’ุจูŽุฑูŽ ูˆูŽุนูŽู†ู’ ู„ูุญููˆู…ู ุงู„ู’ุญูู…ูุฑู ุงู„ุฅูู†ู’ุณููŠู‘ูŽุฉู.
Maโ€™ana:
Hakika Sayyadina Aliyu radhiyallahu anhu ya ji Ibn Abbas radhiyallahu anhuma yana saukakawa akan auren mutuโ€™a, sai ya ce; ka saurara ya Ibn Abbas, lallai Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama ya hana yin auren mutuโ€™a da cin naman jakin gida a ranar Khaibar.
Don haka ba za a kafa hujja da fatarwar Ibn Abbas radhiyallahu anhu ba, domin shi kansa sai daga baya sakon Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama na haramcin auren mutuโ€™a ya isa gare shi.
(B)- Ita Kuwa maganar Jabir Ibn Abdullah radhiyallahu anhuma cewa:
ูƒูู†ู‘ูŽุง ู†ูŽุณู’ุชูŽู…ู’ุชูุนู ุจูุงู„ู’ู‚ูุจู’ุถูŽุฉู ู…ูู†ูŽ ุงู„ุชู‘ูŽู…ู’ุฑู ูˆูŽุงู„ุฏู‘ูŽู‚ููŠู‚ู ุงู„ุฃูŽูŠู‘ูŽุงู…ูŽ ุนูŽู„ูŽู‰ ุนูŽู‡ู’ุฏู ุฑูŽุณููˆู„ู ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู’ ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู…. ูˆูŽุฃูŽุจูู‰ ุจูŽูƒู’ุฑู ุญูŽุชู‘ูŽู‰ ู†ูŽู‡ูŽู‰ ุนูŽู†ู’ู‡ู ุนูู…ูŽุฑู…
Maโ€™ana:
Mun kasance muna mutuโ€™a da cikon tafi na dabino da gari (garin alkama) a zamanin Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama da Sayyadina Abubakar radhiyallahu anhu, har saida Sayyadina Umar radhiyallahu anhu ya hana…
To, a nan za mu ce da su Sayyadina Umar radhiyallahu anhu ya ji hanin auren mutuโ€™a ne daga Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama, shi ya sa ya hana yinsa kamar yadda Sayyadina Aliyu radhiyallahu anhu ya ji haramcin a wajen Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama kuma ya hana Ibn Abbas radhiyallahu anhuma. Wannan dalilin shi ya sa su Jabir ba su ja da Sayyadina Umar radhiyallahu anhu ba, kamar yadda Ibn Abbas radhiyallahu anhu bai ja da Sayyadina Aliyu radhiyallahu anhu ba.
(B)-Kuma koda ma za’a kaddara cewa Abdullahi Ibn Abbas radhiyallahu anhuma da Jabir Ibn Abdullahi radhiyallahu anhuma ba su janye fatawarsu ba har suka mutu, to, ba za a yi aiki da fatawarsu ba, tunda hana yin auren mutuโ€™a ya tabbata daga Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama.
Amma maganar da suka yi cewa: Sayyadina Umar radhiyallahu anhu ya hana yin auren mutuโ€™a ne saboda wata manufa ta siyasa, to, wannan ba abin sallamawa ba ne, domin kuwa Sayyadina Umar radhiyallahu anhu ya yi haka ne don sanarwa da aiwatar da abinda ya ji daga Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama na hana mutu’a. Kamar yadda aka rawaito daga Salim Ibn Abdallah daga babansa radhiyallahu anhu ya ce:
ุตูŽุนูุฏูŽ ุนูู…ูŽุฑู ุงู„ู’ู…ูู†ู’ุจูŽุฑูŽ ููŽุญูŽู…ูุฏูŽ ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ูŽ ูˆูŽุฃูŽุซู’ู†ูŽู‰ ุนูŽู„ูŽูŠู’ู‡ู ุซูู…ู‘ูŽ ู‚ูŽุงู„ูŽ : ู…ูŽุง ุจูŽุงู„ู ุฑูุฌูŽุงู„ู ูŠูŽู†ู’ูƒูุญููˆู†ูŽ ู‡ูŽุฐูู‡ู ุงู„ู’ู…ูุชู’ุนูŽุฉู ูˆูŽู‚ูŽุฏู’ ู†ูŽู‡ูŽู‰ ุฑูŽุณููˆู„ู ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู -ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู…- ุนูŽู†ู’ู‡ูŽุง ู„ุงูŽ ุฃููˆู’ุชูŽู‰ ุจูุฃูŽุญูŽุฏู ู†ูŽูƒูŽุญูŽู‡ูŽุง ุฅูู„ุงู‘ูŽ ุฑูŽุฌูŽู…ู’ุชูู‡ู.
Maโ€™ana:
Sayyadina Umar radhiyallahu anhu ya hau mimbari ya godewa Allah ya yi yabo a gare shi, sannan ya ce: mene ne ya sa wasu mazaje suke yin auren mutuโ€™a, bayan Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama ya hana? To duk wanda aka kawo mini shi ya yi auren mutuโ€™a sai na jefe shi(a matsayin haddi, muddin ya taba aure).
Abinda ke karfafa maganar Sayyadina Umar radhiyallahu anhu shine hadisin da ya zo daga Urwatu Ibn Zubair ya ce:
ุฃูŽู†ู‘ูŽ ุนูŽุจู’ุฏูŽ ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ุจู’ู†ูŽ ุงู„ุฒู‘ูุจูŽูŠู’ุฑู ู‚ูŽุงู…ูŽ ุจูู…ูŽูƒู‘ูŽุฉูŽ ููŽู‚ูŽุงู„ูŽ ุฅูู†ู‘ูŽ ู†ูŽุงุณู‹ุง – ุฃูŽุนู’ู…ูŽู‰ ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ู‚ูู„ููˆุจูŽู‡ูู…ู’ ูƒูŽู…ูŽุง ุฃูŽุนู’ู…ูŽู‰ ุฃูŽุจู’ุตูŽุงุฑูŽู‡ูู…ู’ – ูŠููู’ุชููˆู†ูŽ ุจูุงู„ู’ู…ูุชู’ุนูŽุฉู – ูŠูุนูŽุฑู‘ูุถู ุจูุฑูŽุฌูู„ู – ููŽู†ูŽุงุฏูŽุงู‡ู ููŽู‚ูŽุงู„ูŽ ุฅูู†ู‘ูŽูƒูŽ ู„ูŽุฌูู„ู’ููŒ ุฌูŽุงูู ููŽู„ูŽุนูŽู…ู’ุฑูู‰ ู„ูŽู‚ูŽุฏู’ ูƒูŽุงู†ูŽุชู ุงู„ู’ู…ูุชู’ุนูŽุฉู ุชููู’ุนูŽู„ู ุนูŽู„ูŽู‰ ุนูŽู‡ู’ุฏู ุฅูู…ูŽุงู…ู ุงู„ู’ู…ูุชู‘ูŽู‚ููŠู†ูŽ – ูŠูุฑููŠุฏู ุฑูŽุณููˆู„ูŽ ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ููŽู‚ูŽุงู„ูŽ ู„ูŽู‡ู ุงุจู’ู†ู ุงู„ุฒู‘ูุจูŽูŠู’ุฑู ููŽุฌูŽุฑู‘ูุจู’ ุจูู†ูŽูู’ุณููƒูŽ ููŽูˆูŽุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ู„ูŽุฆูู†ู’ ููŽุนูŽู„ู’ุชูŽู‡ูŽุง ู„ุฃูŽุฑู’ุฌูู…ูŽู†ู‘ูŽูƒูŽ ุจูุฃูŽุญู’ุฌูŽุงุฑููƒูŽ. ู‚ูŽุงู„ูŽ ุงุจู’ู†ู ุดูู‡ูŽุงุจู ููŽุฃูŽุฎู’ุจูŽุฑูŽู†ูู‰ ุฎูŽุงู„ูุฏู ุจู’ู†ู ุงู„ู’ู…ูู‡ูŽุงุฌูุฑู ุจู’ู†ู ุณูŽูŠู’ูู ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ุฃูŽู†ู‘ูŽู‡ู ุจูŽูŠู’ู†ูŽุง ู‡ููˆูŽ ุฌูŽุงู„ูุณูŒ ุนูู†ู’ุฏูŽ ุฑูŽุฌูู„ู ุฌูŽุงุกูŽู‡ู ุฑูŽุฌูู„ูŒ ููŽุงุณู’ุชูŽูู’ุชูŽุงู‡ู ููู‰ ุงู„ู’ู…ูุชู’ุนูŽุฉู ููŽุฃูŽู…ูŽุฑูŽู‡ู ุจูู‡ูŽุง ููŽู‚ูŽุงู„ูŽ ู„ูŽู‡ู ุงุจู’ู†ู ุฃูŽุจูู‰ ุนูŽู…ู’ุฑูŽุฉูŽ ุงู„ุฃูŽู†ู’ุตูŽุงุฑูู‰ู‘ู ู…ูŽู‡ู’ู„ุงู‹. ู‚ูŽุงู„ูŽ ู…ูŽุง ู‡ูู‰ูŽ ูˆูŽุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ู„ูŽู‚ูŽุฏู’ ููุนูู„ูŽุชู’ ููู‰ ุนูŽู‡ู’ุฏู ุฅูู…ูŽุงู…ู ุงู„ู’ู…ูุชู‘ูŽู‚ููŠู†ูŽ. ู‚ูŽุงู„ูŽ ุงุจู’ู†ู ุฃูŽุจูู‰ ุนูŽู…ู’ุฑูŽุฉูŽ ุฅูู†ู‘ูŽู‡ูŽุง ูƒูŽุงู†ูŽุชู’ ุฑูุฎู’ุตูŽุฉู‹ ููู‰ ุฃูŽูˆู‘ูŽู„ู ุงู„ุฅูุณู’ู„ุงูŽู…ู ู„ูู…ูŽู†ู ุงุถู’ุทูุฑู‘ูŽ ุฅูู„ูŽูŠู’ู‡ูŽุง ูƒูŽุงู„ู’ู…ูŽูŠู’ุชูŽุฉู ูˆูŽุงู„ุฏู‘ูŽู…ู ูˆูŽู„ูŽุญู’ู…ู ุงู„ู’ุฎูู†ู’ุฒููŠุฑู ุซูู…ู‘ูŽ ุฃูŽุญู’ูƒูŽู…ูŽ ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ุงู„ุฏู‘ููŠู†ูŽ ูˆูŽู†ูŽู‡ูŽู‰ ุนูŽู†ู’ู‡ูŽุง
Maโ€™ana:
Abdullahi Ibn Zubair radhiyallahu anhu ya mike a Makka yana mai huduba sai ya ce: โ€œhakika wasu mutane Allah ya makantar da zukatansu kamar yadda ya makarantar da idanunsu, suna ba da fatawa da yin auren mutuโ€™a”. Yana yin shagube ne ga wani mutum. Sai (Abdullahi Ibn Abbas radhiyallahu anhu) ya kirawo shi ya ce: lallai kai mai kausasa harshe ne, wallahi mutuโ€™a ta kasance ana yin ta a zamanin Shugaban masu takawa (wato. Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama). Sai Ibn Zubair radhiyallahu anhu ya ce: to kai ka je ka yi mutuโ€™ar mana, to, wallahi idan kuwa ka yi sai na sanya an jefeka da duwatsu(a matsayin haddi). Sai Ibn Shihab ya ce: “Khalid Ibn Muhajir ya ba ni labari cewa: yayin da yake zaune a wajen wani mutum, sai wani mutum ya zo masa ya tambaye shi halaccin auren mutuโ€™a, sai ya ba shi fatawa da yin sa, sai Ibn Abi Amratal Ansariy radhiyallahu anhu yace da shi; ka bi a hankali! Sai ya ce: mece ce ita? Na rantse da Allah an yi ta a zamanin Shugaban masu takawa, sai Ibn Abi Amr radhiyallahu anhu ya ce: ai ita(mutuโ€™a) rangwame ce a farkon Musulunci ga wanda ya matsu kamar yadda aka halatta mushe da jini da naman alade ga wanda ya matsu. Sannan bayan Musulunci ya cika sai aka haramta ta”.
3- Ita kuwa hujjarsu ta hankali cewa: auren mutuโ€™a amfani ne kubutacce daga muni, ba abin da hankali mai kyau zai sallama masa ba ne, domin kuwa ita ce mafi tsantsar cutarwa ga macen da aka yi mutuโ€™a da ita da kuma dan da ta haifa ta hanyar mutuโ€™a; saboda duk matar da take bayar da kanta ga mazaje barkatai su sadu da ita da sunan mutuโ€™a, ko shakka babu za ta wayi gari da ‘ya ‘ya an tafi an barta da su barkatai, Idan ba haka ba, ta fuskanci barazanar zubar da cikin, kuma maza za su rika gudar auren ta aure na hakika, don haka za ta sami kanta cikin kaskanci a idanun jamaโ€™a, sannan kuma, kowa yana iya neman saduwa da ita kamar karuwa. Haka kuma dan da ta haifa zai wayi gari ba shi da uba, ana yi masa kallon dan zina, don mai auren mutuโ€™a ba ya so a jingina masa dan da aka haifa a dalilin mutuโ€™ar. Kuma auren mutuโ€™a, ana yin sane kawai don shaโ€™awa, ba don samun zuriya ba. Sannan kuma babu rahama ballantana tausayin da Allah ya sanya a tsakanin maโ€™aurata wadanda suke saukaka rabuwa bayan an yi aure. Haka kuma matar da aka yi mutuโ€™a da ita ba ta takaba ballantana iddar da Ubangiji subhanahu wa ta’ala ya yi umarni da yin su.
Haka kuma duk hujjar da aka kafa da hankali ta sabawa nassi, to, ba za a yi laโ€™akari da ita ba.
4- Dangane da maganar ijmaโ€™in Ahlulbaiti a kan auren mutuโ€™a kuwa, bai tabbata ba,
A)- domin sanannen abu ne cewa Zaidu Ibn Aliyu yana tare da Jumhurun malamai a bisa haramcin auren mutuโ€™a, ga shi kuma yana daga cikin manyan Ahlulbaiti.
B)-Sannan ga Sayyadina Aliyu radhiyallahu anhu wanda shi ne kololuwa a cikin shugabannin Ahlulbaiti shima ya haramta auren mutuโ€™a, kamar yadda hadisi ya gabata.
Bari ma shi ne wanda ya rawaito hadisin da ke hana auren mutuโ€™a a yakin Khaibar.
C)- Sannan an rawaito daga Abdullahi Ibn Sinan ya ce:
Na tambayi Abu Abdullahi (Ja’afarus Sadik) alaihis salam dangane da hukuncin mutuโ€™a, sai ya ce: kar ka kuskura ka kazanta kanka da ita.
D)- Haka kuma an rawaito daga Ammar ya ce : Abu Abdullahi alaihis salam ya ce da ni da Sulaiman bn Khalid: hakika an haramta auren mutuโ€™aโ€.
E)- kuma Aliyu bn Yakzin ya tambayi Abu Hassan alaihis salam a kan mutuโ€™a, sai ya ba shi amsa cewa : Mene ne ya hada ka da mutuโ€™a? Allah ya wadatar da kai ga barintaโ€.
Wannan ne ya sanya babban malamin nan na Malikiyya wato Hafiz Ibn Abdulbar ya ce:
Malamai sun hadu akan cewa : โ€œauren mutuโ€™a haramun neโ€ daga cikin su akwai Imam Malik da almajiransa, da manyan malaman Madina da Sufyanus Sauri da Abu Hanifa daga malaman Kufa da Imamus Shafiโ€™i da Imamul Lais bn Saโ€™ad daga malaman Misra da Magrib da Auzaโ€™i daga cikin Manyan malaman Sham, da Imam Ahmad bn Hanbal da Ishak da Abu Saur da abu Ubaidah da Dawuduz Zahiri da Imamud Dabari, dukkansu sun tafi a kan haramcin auren mutuโ€™a.
Dalilansu kuwa su ne:
i- fadin Ubangiji subhanahu wa ta’ala cewa:
ูˆูŽุงู„ู‘ูŽุฐููŠู†ูŽ ู‡ูู…ู’ ู„ูููุฑููˆุฌูู‡ูู…ู’ ุญูŽุงููุธููˆู†ูŽ (29) ุฅูู„ู‘ูŽุง ุนูŽู„ูŽู‰ ุฃูŽุฒู’ูˆูŽุงุฌูู‡ูู…ู’ ุฃูŽูˆู’ ู…ูŽุง ู…ูŽู„ูŽูƒูŽุชู’ ุฃูŽูŠู’ู…ูŽุงู†ูู‡ูู…ู’ ููŽุฅูู†ู‘ูŽู‡ูู…ู’ ุบูŽูŠู’ุฑู ู…ูŽู„ููˆู…ููŠู†ูŽ (30) ููŽู…ูŽู†ู ุงุจู’ุชูŽุบูŽู‰ ูˆูŽุฑูŽุงุกูŽ ุฐูŽู„ููƒูŽ ููŽุฃููˆู„ูŽุฆููƒูŽ ู‡ูู…ู ุงู„ู’ุนูŽุงุฏููˆู†ูŽ (31) ุงู„ู…ุนุง ุฑุฌ: 31 – 29
Maโ€™ana:
(Hakika muminai) sune wadanda suke kiyaye farjinsu. Saifa ga matayensu, ko kuma abin da suka mallaka na kuyangi, hakika su ba abin zargi ba ne. Wanda ya nemi (wani abu) koma bayan wancan, wadannan sune suka ketare dokokin Allah…..
Dalili a cikin wannan aya shi ne; bai halatta mutum ya sadu da wata mace ba, sai matarsa ta aure ko kuyangar da ya mallaka kamar yadda ya gabata.
Ita kuwa wadda ake zaman mutuโ€™a da ita, ba matar auren da shariโ€™a ta yarda da ita ba ce kuma ba kuyanga ba ce, kuma yin hakan bayan haramta shi, ketare dokokin Allah ne. Dalilan da suke karfafa cewa matar mutuโ€™a ba matar aure ba ce, kuma ba kuyangar da aka mallaka ba ce su ne:
a)- Idan matarsa ce da sun gaji junansu(idan daya a cikin su ya rasu kafin karewar muddar su). Saboda fadin Ubangiji subhanahu wa ta’ala cewa:
ูˆูŽู„ูŽูƒูู…ู’ ู†ูุตู’ูู ู…ูŽุง ุชูŽุฑูŽูƒูŽ ุฃูŽุฒู’ูˆูŽุงุฌููƒูู…ู’ ุฅูู†ู’ ู„ูŽู…ู’ ูŠูŽูƒูู†ู’ ู„ูŽู‡ูู†ู‘ูŽ ูˆูŽู„ูŽุฏูŒโ€ฆ ุงู„ู†ุณุงุก: 12
Maโ€™ana:
Kuma kuna da rabin abin da matanku suka bari, idan sun kasance ba su da `ya`ya…
b)- Kuma idanda matarsa ce sai a tabbatar masa da dan da ta haifa ta hanyar mutuโ€™ar, saboda fadin Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama cewa:
ุงู„ูˆู„ุฏ ู„ู„ูุฑุงุด ูˆู„ู„ุนุงู‡ุฑ ุงู„ุญุฌุฑ
Maโ€™ana:
Da ana danganta shi ne zuwa ga ubansa (idan har matar aure ce ko sadaka), amma wanda ya yi zina da matar aure ko sadaka har ta yi ciki, to, shariโ€™a ta hana shi wannan dan*.
Amma masu daโ€™awar yin auren mutuโ€™a, ba’ma’ sa son danganta dan mutuโ€™a zuwa ga ubansa, saboda matar da aka yi mutuโ€™ar da ita ba ta zama matar firash (matar aure) ba.
c)- Haka kuma idanda matarsa ce da za ta yi masa idda, idan sun rabu ko ya mutu, domin matan aure na shari’a sune Allah ya hukuntawa wadannan al’amuran, amma babu idda a cikin auren mutuโ€™a.
Duk wadannan hukunce-hukuncebabu nassi infantacce da ya kebance matar mutu’a; wanda hakan ya nuna ita ba matar aure ba ce. Ita wata rukusa ce da musulunci yayi a wani lokaci kafin a haramta ta. Kamar yadda giya ba a haramta ta rana daya ba, amma haramcinta a yanzu har tashin kiyama ne.
iii)- Dalilansu kuma daga sunna su ne kamar haka;
1- Hadisin da ya tabbata daga Sayyadina Aliyu radhiyallahu anhu na hana auren mutuโ€™a a Khaibar, kamar yadda ya gabata cewa:
ุฃูŽู†ู‘ูŽ ุฑูŽุณููˆู„ูŽ ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ู†ูŽู‡ูŽู‰ ุนูŽู†ู’ ู…ูุชู’ุนูŽุฉู ุงู„ู†ู‘ูุณูŽุงุกู ูŠูŽูˆู’ู…ูŽ ุฎูŽูŠู’ุจูŽุฑูŽ ูˆูŽุนูŽู†ู’ ุฃูŽูƒู’ู„ู ู„ูุญููˆู…ู ุงู„ู’ุญูู…ูุฑู ุงู„ุฅูู†ู’ุณููŠู‘ูŽุฉู.
Maโ€™ana:
Hakika Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama ya hana yin auren mutuโ€™a da cin naman jakin gida a ranar yakin Khaibar.
2- Hadisin da ya tabbata daga Rabiโ€™i Ibn Sabrata radhiyallahu anhu ya ce:
ุฃูŽุฐูู†ูŽ ู„ูŽู†ูŽุง ุฑูŽุณููˆู„ู ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ุจูุงู„ู’ู…ูุชู’ุนูŽุฉู ููŽุงู†ู’ุทูŽู„ูŽู‚ู’ุชู ุฃูŽู†ูŽุง ูˆูŽุฑูŽุฌูู„ูŒ ุฅูู„ูŽู‰ ุงู…ู’ุฑูŽุฃูŽุฉู ู…ูู†ู’ ุจูŽู†ูู‰ ุนูŽุงู…ูุฑู ูƒูŽุฃูŽู†ู‘ูŽู‡ูŽุง ุจูŽูƒู’ุฑูŽุฉูŒ ุนูŽูŠู’ุทูŽุงุกู ููŽุนูŽุฑูŽุถู’ู†ูŽุง ุนูŽู„ูŽูŠู’ู‡ูŽุง ุฃูŽู†ู’ููุณูŽู†ูŽุง ููŽู‚ูŽุงู„ูŽุชู’ ู…ูŽุง ุชูุนู’ุทูู‰ ููŽู‚ูู„ู’ุชู ุฑูุฏูŽุงุฆูู‰. ูˆูŽู‚ูŽุงู„ูŽ ุตูŽุงุญูุจูู‰ ุฑูุฏูŽุงุฆูู‰. ูˆูŽูƒูŽุงู†ูŽ ุฑูุฏูŽุงุกู ุตูŽุงุญูุจูู‰ ุฃูŽุฌู’ูˆูŽุฏูŽ ู…ูู†ู’ ุฑูุฏูŽุงุฆูู‰ ูˆูŽ ูƒูู†ู’ุชู ุฃูŽุดูŽุจู‘ูŽ ู…ูู†ู’ู‡ู ููŽุฅูุฐูŽุง ู†ูŽุธูŽุฑูŽุชู’ ุฅูู„ูŽู‰ ุฑูุฏูŽุงุกู ุตูŽุงุญูุจูู‰ ุฃูŽุนู’ุฌูŽุจูŽู‡ูŽุง ูˆูŽุฅูุฐูŽุง ู†ูŽุธูŽุฑูŽุชู’ ุฅูู„ูŽู‰ู‘ูŽ ุฃูŽุนู’ุฌูŽุจู’ุชูู‡ูŽุง ุซูู…ู‘ูŽ ู‚ูŽุงู„ูŽุชู’ ุฃูŽู†ู’ุชูŽ ูˆูŽุฑูุฏูŽุงุคููƒูŽ ูŠูŽูƒู’ูููŠู†ูู‰. ููŽู…ูŽูƒูŽุซู’ุชู ู…ูŽุนูŽู‡ูŽุง ุซูŽู„ุงูŽุซู‹ุง ุซูู…ู‘ูŽ ุฅูู†ู‘ูŽ ุฑูŽุณููˆู„ูŽ ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ู ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ู‚ูŽุงู„ ู…ูŽู†ู’ ูƒูŽุงู†ูŽ ุนูู†ู’ุฏูŽู‡ู ุดูŽู‰ู’ุกูŒ ู…ูู†ู’ ู‡ูŽุฐูู‡ู ุงู„ู†ู‘ูุณูŽุงุกู ุงู„ู‘ูŽุชูู‰ ูŠูŽุชูŽู…ูŽุชู‘ูŽุนู ููŽู„ู’ูŠูุฎูŽู„ู‘ู ุณูŽุจููŠู„ูŽู‡ูŽุง.
Maโ€™ana
Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama ya yi mana izinin yin auren mutuโ€™a ranar fatโ€™hu Makka, sai na tafi ni da wani mutum zuwa wata mace daga kabilar Banu Amir kamar budurwar (Kabilar Aizaโ€™a) sai muka bijirar da kanmu gare ta domin mu yi mutuโ€™a da ita, sai ta ce; mai za ku ba ni? Sai na ce bargona, sai abokina ma ya ce: bargonsa, bargon abokin nawa ya fi kyau, ni kuma na fi shi samartaka, idan ta dubi bargon abokina sai ya burgeta, idan kuma ta dube ni sai samartakata ta burgeta, sai ta ce: kai da bargonka kun ishe ni, sai muka zauna tare da ita kwana uku, sannan sai Annabi sallallahu alaihi wa sallama ya ce: duk wanda yake tare da matar mutuโ€™a, to, ya rabu da ita.
A wata ruwayar kuma Rabiโ€™u Ibn Sabratal Juhani ya ce:
ุฃูŽู†ู‘ูŽ ุฃูŽุจูŽุงู‡ู ุญูŽุฏู‘ูŽุซูŽู‡ู ุฃูŽู†ู‘ูŽู‡ู ูƒูŽุงู†ูŽ ู…ูŽุนูŽ ุฑูŽุณููˆู„ู ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ ุตู„ู‰ ุงู„ู„ู‡ ุนู„ูŠู‡ ูˆุณู„ู… ููŽู‚ูŽุงู„ูŽ ูŠูŽุง ุฃูŽูŠู‘ูู‡ูŽุง ุงู„ู†ู‘ูŽุงุณู ุฅูู†ู‘ูู‰ ู‚ูŽุฏู’ ูƒูู†ู’ุชู ุฃูŽุฐูู†ู’ุชู ู„ูŽูƒูู…ู’ ููู‰ ุงู„ุงูุณู’ุชูู…ู’ุชูŽุงุนูู…ูู†ูŽ ุงู„ู†ู‘ูุณูŽุงุกู ูˆูŽุฅูู†ู‘ูŽ ุงู„ู„ู‘ูŽู‡ูŽ ู‚ูŽุฏู’ ุญูŽุฑู‘ูŽู…ูŽ ุฐูŽู„ููƒูŽ ุฅูู„ูŽู‰ ูŠูŽูˆู’ู…ู ุงู„ู’ู‚ููŠูŽุงู…ูŽุฉู ููŽู…ูŽู†ู’ ูƒูŽุงู†ูŽ ุนูู†ู’ุฏูŽู‡ู ู…ูู†ู’ู‡ูู†ู‘ูŽ ุดูŽู‰ู’ุกูŒ ููŽู„ู’ูŠูุฎูŽู„ู‘ู ุณูŽุจููŠู„ูŽู‡ุง ูˆูŽู„ุงูŽ ุชูŽุฃู’ุฎูุฐููˆุง ู…ูู…ู‘ูŽุง ุขุชูŽูŠู’ุชูู…ููˆู‡ูู†ู‘ูŽุดูŽูŠู’ุฆู‹ุง.
Maโ€™ana:
Lallai babansa (Sabratal Juhanฤซ radhiyallahu anhu) ya ba shi labarin cewa: Hakika sun kasance tare da Manzon Allah sallallahu alaihi wa sallama sai ya ce: Ya ku mutane! Hakika da na yi muku izinin yin mutuโ€™a, amma yanzu Allah ya haramta ta har zuwa ranar alkiyama, saboda haka duk wanda yake tare da matar mutu’a, to, ya sallame ta, kuma kada ku karbi komai daga abin da kuka ba su.
iv)- Dalilinsu na hankali sun ce: Aure ana yin sane don wasu manufofi, ba wai don shaโ€™awa kadai ba, auren mutuโ€™a kuwa babu wadannan manufofin a cikinsa, sai dai kawai biyawa kai bukata ta shaโ€™awa.
v)- Dalilinsu na ijmaโ€™i; suka ce: Hakika alโ€™ummar musulmi sun tafi a kan haramcin auren mutuโ€™a tunda Allah da Manzonsa sallallahu alaihi wa sallama sun hana yinsa tun a ranar fatโ€™hu Makka har zuwa ranar tashin Akiyama, don haka ya zama dole a hanu, ba kuma za a saurari maganar kowa ba. Allah ya fahimtar da masu yi su dena.
Kuna iya neman wannan littafi da na wallafa mai suna “Tsarabar ma’aurata” don Karin fa’idoji da kuma mara’ji’i. Wa sallallahu wa sallama ala Nabiyyina Muhammad wa ala a’lihi wa sahbihi ajma’iin.

Leave a Reply

Latest updates
Categories
%d bloggers like this: