Allah yana bada duniya ga wanda yakeso da wanda baya so

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Da yawa daga cikin mutane idan yaga Allah ya bashi dukiya da lafiya sai ya rinƙa tunanin Cewa son da Allah yake yi masa ne shiyasa ya sami wannan, haka nan idan yaga wani Allah ya jarrabeshi da talauci ko rashin lafiya ko wasu nau’uka na jarabawa sai ya rinƙa ganin kaman Allah baya son wannan ɗin, ko kuma ya tsaɓa wa Allah ne shiyasa Allah ya jarrabeshi.

To abin sam ba haka yake ba, Allah yakan jaraba bayinsa gwargwadon Imaninsu shiyasa Wa’inda sukafi kowa samun Jarabawa sune Annabawa sai wa’inda suke biye dasu wurin riƙo da Addini kamar yadda Annabi Sallallahu alaihi Wasallama ya bada labari.

Ita duniya Allah yana bada ita ga wanda yake so da ma wanda baya so, domin ita duniya bata da wani ƙima a wurin Allah, ita gida ce ta jarabawa, kamar Mutum ne yaje makaranta, zai yi ta shan wahala domin ya fita da Sakamako mai kyawu, toh haka nan duniya idan mutum yayi haƙuri, yayi abinda aka umarce shi dashi gwargwadon iko toh Allah zai taimakeshi a rayuwarsa, sannan kuma daga ƙarshe zai samu Sakamako mai kyawu. Allah yasa mudace.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

One response to “Allah yana bada duniya ga wanda yakeso da wanda baya so”
  1. Umar Badamasi Salisu Avatar
    Umar Badamasi Salisu

    Allah ya taimakemu gaba daya

Leave a Reply

Latest updates
Categories