DORA DAMA A KAN HAGU CIKIN SALLA SHI NE SUNNAH, SAKIN HANNAYE CIKIN SALLA SABANIN SUNNAH NE(Dr Ibrahim Jalo Jalingo)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Imamush Shaukaanii ya ce cikin
littafinsa Nailul Autaar 2/205:
((Hadithan dora dama a kan hagu
ishrin ne suka zo daga Annabi mai
tsira da amincin Allah ta hanyar
mutum goma sha takwas, tsakanin
Sahabi da Tabi’i)).
Ga wasu daga cikin hadithan da
Imamush Shaukaanii ya yi
maganarsu:-
1- Imamu Muslim ya ruwaito hadthi
na 401 cewa: Annabi mai tsira da
amincin Allah: ((Ya kasance yana
dora hannun damansa a kan
hagunsa)).
2- Imamul Bukharii ya ruwaito
hadithi na 740 da Imam Malik cikin
Muwattaa hadithi na 546 cewa
Manzon Allah mai tsira da amincin
Allah yana umurtan sahabbansa
da dora dama a kan hagu:
((Mutane sun kasance ana
umurtan su da cewa: mutum ya
dora damansa a kan zira’insa na
hagu a cikin Salla)).
3- Imamut Tabaraanii ya ruwaito
cikin Almu’ujamul Kabiir hadithi na
11,323, da Imamud Daara Qudnii
cikin Babun Fi Akhzish Shimaal Bil
Yamiin hadithi na 3, da Imam Ibnu
Hibbaan dadithi na 1,770, da Imam
Sulaimaan Ibnu Dawud Attayaalisii
cikin Musnad hadithi na 2,776
cewa Annabi mai tsira da amincin
Allah ya kasance yana cewa: ((Mu
taron Annabawa an umurce mu da
gauggauta buda-baki, da jinkirta
sahur, da kuma mu dora
hannayenmu na dama a kan
hannayenmu na hagu)). Albaanii
ya inganta hadithin cikin Sahihul
Jami’is Sagiir 1/454.
4- Imam Ahmad ya ruwaito hadithi
na 15,090, da Imam Abu Dawud
Hadiyhi na 755, da isnadi sahihi
cewa Manzon Allah mai tsira da
amincin Allah ((Ya wuce wani
mutum yana salla amma ya dora
hannunsa na hagu a kan na dama,
sai ya balle hannun ya dora daman
a kan hagun)).
5- Imam Abu Dawud ya ruwaito
hadithi na 727, da Imam Nasa’ii
hadithi na 963, da Imam Ibnu
Khuzaimah hadithi na 480 da
isnadi sahihi cewa Manzon Allah
mai tsira da amincin Allah ((Ya
kasance yana dora dama a kan
bayan tafinsa na hagu, da kuma
wuyan hannu, da dantse)).
6- Imama Abu Dawud ya ruwaito
hadithi na 759, da Imam Ibnu
Khuzaimah hadithi na 479 cewa
Annabi mai tsira da amincin Allah
((Ya kasance yana sanya hannun
damansa a kan hagunsa, sannan
sai ya hada tsakaninsu a kan
kirjinsa alhalin yana cikin salla)).
TAMBAYOYI TARE DA
AMSOSHINSU:
(1) Idan wani ya ce: Amma kuma ai
Imamut Tabarii ya ruwaito cikin
littafinsa Almuujamul Kabiir hadithi
na 16,563, daga Sahabi Mu’azu
Dan Jabal ya ce:-
(( ﻛﺎﻥ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺍﺫﺍ ﻛﺎﻥ ﻓﻲ
ﺻﻼﺗﻪ ﺭﻓﻊ ﻳﺪﻳﻪ ﻗﺒﺎﻟﺔ ﺃﺫﻧﻴﻪ، ﻓﺈﺫﺍ ﻛﺒﺮ ﺍﺭﺳﻠﻬﻤﺎ، ﺛﻢ
ﺳﻜﺖ، ﻭﺭﺑﻤﺎ ﻳﻀﻊ ﻳﻤﻴﻨﻪ ﻋﻠﻰ ﻳﺴﺎﺭﻩ )).
Ma’ana: ((Annabi mai tsira da
amincin Allah ya kasance idan
yana cikin sallarsa sai ya daga
hannu daura da kunnensa, idan ya
yi kabbara sai ya sake su, sai
kuma ya yi shiru, wani lokaci ma
nakan gan shi yana dora damansa
a kan hagunsa)). Wannan hadithi
ai shi ne hujjar sake hannu!!
Sai a ce da shi: Da farko dai ya
kamata ka san cewa wannan
hadithi maudhuu’i ne, watau
hadithi ne da cikin isnadinsa akwai
makaryaci kazzaabi wannan kuwa
shi ne: Khasiib Bin Jahdar, ya zo
cikin littafin Miizaanu Litidaal 1/653
kamar haka:-
(( ﺍﻟﺨﺼﻴﺐ ﺑﻦ ﺟﺤﺪﺭ: ﻋﻦ ﻋﻤﺮﻭ ﺑﻦ ﺩﻳﻨﺎﺭ، ﻭﺃﺑﻲ
ﺻﺎﻟﺢ ﺍﻟﺴﻤﺎﻥ، ﻛﺬﺑﻪ ﺷﻌﺒﺔ ﻭﺍﻟﻘﻄﺎﻥ ﻭﺍﺑﻦ ﻣﻌﻴﻦ.
ﻭﻗﺎﻝ ﺍﺣﻤﺪ: ﻻ ﻳﻜﺘﺐ ﺣﺪﻳﺜﻪ. ﻭﻗﺎﻝ ﺍﻟﺒﺨﺎﺭﻱ: ﻛﺬﺍﺏ
ﺍﺳﺘﻌﺪﻯ ﻋﻠﻴﻪ ﺷﻌﺒﺔ)).
Ma’ana: ((Khasiib Bin Jahdar: daga
Amr Bin Diinaar, da Abu Salihis
Sammaan: Shu’ubah, da Qattaan,
da Ibnu Ma’iin sun karyata shi.
Ahmad ya ce: Ba a rubuta
hadithinsa. Bukharii ya ce:
Makaryaci ne, Shu’ubah ya yi
bayanin karyarsa))
Na biyu: Da za a kaddara cewa
hadithin ingantacce ne, to da sai a
fassara shi da cewa: yana nufin
bayan Annabi ya daga
hannayensa daura da kunnuwansa
lokacin kabbarar harama, ya kan
sake hannayen nasa ne zuwa
kirjinsa, dole a yi irin wannan
fassarar saboda hadithin ya dace
da sauran hadithai ingantattu cikin
babin.
Babban masanin ilmin hadithi
Alhaafiz Ibnu Hajar ya ce cikin
littafinsa: Attalkhiisul Habiir 1/554:-
(( ﺗﻨﺒﻴﻪ: ﻗﺎﻝ ﺍﻟﻐﺰﺍﻟﻲ: ﺳﻤﻌﺖ ﺑﻌﺾ ﺍﻟﻤﺤﺪﺛﻴﻦ
ﻳﻘﻮﻝ: ﻫﺬﺍ ﺍﻟﺨﺒﺮ ﺍﻧﻤﺎ ﻭﺭﺩ ﺑﺎﻧﻪ ﻳﺮﺳﻞ ﻳﺪﻳﻪ ﺍﻟﻰ
ﺻﺪﺭﻩ، ﻻ ﺍﻧﻪ ﻳﺮﺳﻠﻬﻤﺎ ﺛﻢ ﻳﺴﺘﺄﻧﻒ ﺭﻓﻌﻬﻤﺎ ﺍﻟﻰ
ﺍﻟﺼﺪﺭ. ﺣﻜﺎﻩ ﺍﺑﻦ ﺍﻟﺼﻼﺡ ﻓﻲ ﻣﺸﻜﻞ ﺍﻟﻮﺳﻴﻂ )).
Ma’ana: ((Fadakarwa: Gazaalii ya
ce: Na ji sashin malaman hadithi
na cewa: Wannan hadithi ya zo ne
a kan cewa yana sake hannayensa
ne zuwa girjinsa, ba wai yana sake
su ba ne, sannan daga baya ya
daga su zuwa girji ba. Ibnus
Salaah ya hikaito shi cikin
“Mushkilul Wasiit”)).
(2) Idan wani kuma ya ce: To ai an
samu daga cikin magabata
wadanda suka yi salla hannayensu
a sake, don mene ne za a ce da
mu yanzu: ba za mu yi salla
hannayenmu a sake ba?
To sai a ce da shi: Na farko dai ya
kamata ka san cewa ya kai
dan’uwa! Annabi Muhammad mai
tsira da amincin Allah shi ne kadai
wanda Allah Ya aiko shi zuwa gare
ka, bai aiko waninsa zuwa gare ka
ba a matsayin manzo, saboda
haka ba daidai ba ne ka bar
umurninsa shi Annabi Muhammad
ko kuma ka bar aikinsa, sannan ka
je kana riko da umurni ko da aikin
wani koma wane ne shi a wannan
duniya!
Abu na biyu: A lokacin da Sahabi
Abdullahi Dan Abbas ya yi
yunkurin tabbatar da sunnar
tamattu’i cikin Hajji, an samu wasu
mutane da suka ce da shi: Ai
Abubakar da Umar sun hana
Mut’ar Hajji, shi kuwa sai ya amsa
ya ce da su: ((Wani dutse ya yi
kusan sauko muku daga sama! Ina
ce muku: Manzon Allah mai tsira
da amincin Allah ya ce, sannan
kuna ce da ni: Abubakar da Umar
sun ce!)).
Wannan magana ta Abdullahi Dan
Abbas asalinta na cikin Musnadu
Ahmad hadithi na 3,121, da
Almuujamul Ausat na Tabaraanii
hadithi na 21, da Jami’u bayanil
ilmi na Ibnu Abdil Bar hadithi na
2,377, da Alfaqih wal Mutafaqqih
na Khatiibul Bagdaadii hadithi na
380.
Abu na uku shi ne: Barin aiki da
maganar Annabi ko aikinsa zuwa
yin aiki da maganar wani ko
aikinsa saba wa Ijma’in Al’ummah
ne, shi kuwa yin hakan haramun
ne a bisa ittifakin dukkan malaman
Duniya, idan Annabi ya yi umurni
da a yi Kablu a cikin salla sannan
ka ji wani kuma yana cewa a yi
sadlu domin ai sadlu ba ya bata
salla to lalle wannan mutum ya yi
haramun ya zama mai sabon Allah
a bisa ijma’in Maluman Musulunci!
Ya zo cikin littafin Iiqazul Himam
shafi na 68 cewa Imamush Shafi’ii
ya ce: ((Musulmi sun yi Ijma’i a kan
cewa duk wanda sunnar Manzon
Allah mai tsira da amincin Allah ta
bayyana gare shi, to, ba ya halatta
gare shi ya bar ta saboda yin riko
da maganar wani)).
(3) Idan wani ya ce: To ai sake
hannaye cikin salla shi ne
mazhabar Imam Malik, tunda mu
kuwa Malikiyyah ne ke nan dukkan
abin da Imam Malik ya yi na Addini
shi ne mu ma za mu yi!!
To sai a ce da shi: Na farko dai ya
kamata ka san cewa Allah
Madaukakin Sarki bai aiko maka
Imam Malik a matsayin manzo ba,
a’a Ya aiko maka Annabi
Muhammad ne a matsayin manzo
zuwa gare ka kai da sauran
mutanen Duniya baki daya, shi
kuwa Annabi Muhammad babu
inda ya ce da kai ka yi salla
hannayenka a sake, a’a abin da ya
ce da kai shi ne: Ka dora damanka
a kan hagunka cikin sallanka. Ta
kaka za ka bar nasa ka riki na wani
komin girmansa kuwa a idanunka?
A bu na biyu: cewa da ka yi:
mazhabar Imam Malik ita ce: yin
salla hannaye a sake, magana ce
mara dikka, saboda shi Imam Malik
yana da fatawowi daidai har guda
hudu ne cikin wannan mas’alar, ba
wai fatawa daya kawai ba.
Babban Malami cikin mazhabar
malikiyyah Imamul Baajii ya ce
cikin littafinsa Almuntaqaa 1/281:
Imam Malik yana da fatawowi hudu
da aka ruwaito daga gare shi cikin
wannan mas’alar: Fatawar farko:
Ash’hab ya ruwaito daga gare shi
cewa: Babu laifi a dora dama a kan
hagu cikin sallar nafila da farilla.
Fatawa ta biyu: Mutarrif da Ibnul
Maajishuun da kuma almajiransa
na Iraq sun ruwaito daga gare shi
cewa: Dora dama a kan hagu cikin
salla mustahabbi ne. Fatawa ta
uku: Mutanen Iraq sun ruwaito
daga Malikawa daga shi Imam
Malik cewa: Kada a dora dama a
kan hagu cikin salla. Fatawa ta
hudu: Ibnul Qaasim ya ruwaito
daga gare shi cewa: makruuhi ne a
dora dama a kan hagu cikin sallar
farilla, amma babu laifi a yi hakan
cikin sallar nafila.
A nan ai kun ga ya kamata a ce
imma Malikiyyar za a yi, to sai a yi
wacce ta dace da sunnar Annabi
mai tsira da amincin Allah, ba wai
wacce ta saba wa sunnar
Muhammadur Rasuulul Lahi ba,
Allah ya taimake kan yin aiki da
sahihiyar Sunnar ManzonSa.
(4) Idan wani ya ce: To mene ne
fahimtar Malamanmu na Da’awah
da Aqidah kuma cikin wannan
mas’alar?
Sai a ce da shi: Fahimtar mutanen
da muka sani daga cikinsu ita ce:
Yin salla hannaye a sake abu ne
da yake sabanin Sunnah. Misali:
Sheik Abdulaziz Bin Baz ya ce
cikin littafinsa na fatawa 11/144:-
(( ﺍﻟﺜﺎﺑﺖ ﻋﻦ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ ﺍﻧﻪ
ﻳﻘﺒﺾ ﻳﺪﻳﻪ ﺣﺎﻝ ﻗﻴﺎﻣﻪ ﻓﻲ ﺍﻟﺼﻼﺓ… ﺍﻣﺎ ﺇﺭﺳﺎﻝ
ﺍﻟﻴﺪﻳﻦ ﻓﻲ ﺍﻟﺼﻼﺓ ﻓﻤﻜﺮﻭﻩ ﻻ ﻳﻨﺒﻐﻲ ﻓﻌﻠﻪ ﻟﻜﻮﻧﻪ
ﺧﻼﻑ ﺍﻟﺴﻨﺔ )).
Ma’ana: ((Abin da ya tabbata daga
Annabi mai tsira da amincin Allah
shi ne cewa: Yana kame
hannayensa ne lokacin da yake
tsaye cikin salla ..Amma sake
hannaye a cikin salla makruhi ne,
yin sa bai kamata ba, saboda
kasancewarsa sabanin Sunnah)).
Sannan ya sake cewa cikin
wannan littafin nasa 11/145:-
(( ﻭﺑﻤﺎ ﺫﻛﺮﻧﺎﻩ ﺗﻌﻠﻤﻮﻥ ﺍﻥ ﺇﺭﺳﺎﻝ ﺍﻟﻴﺪﻳﻦ ﻻ ﻳﻘﺪﺡ
ﻓﻲ ﺍﺳﻼﻡ ﺍﻟﻤﺴﻠﻢ، ﻭﻻ ﻓﻲ ﺍﻛﻞ ﺫﺑﻴﺤﺘﻪ ﻟﻜﻨﻪ ﻣﻜﺮﻭﻩ
ﻭﻣﺨﺎﻟﻒ ﻟﻠﺴﻨﺔ ﻻ ﻳﻨﺒﻐﻲ ﻓﻌﻠﻪ )).
Ma’ana: ((Saboda abin da muka
ambata din nan ne za ku san
cewa: Sake hannaye ba ya soke
Musuluncin Musulmi, haka nan cin
yankansa, sai dai kuma shi
makruhi ne, kuma abu ne da ya
saba wa Sunnah, ba ya kamata a
yi shi)).
Sannan ya sake cewa cikin
wannan littafi nasa 29/239:-
(( ﻫﺬﺍ ﻣﻜﺮﻭﻩ، ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ ﺿﻤﻬﻤﺎ ﻭﺟﻌﻠﻬﻤﺎ ﻋﻠﻰ
ﺍﻟﺼﺪﺭ، ﻭﺟﻌﻞ ﺍﻟﻴﻤﻨﻰ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﻴﺴﺮﻯ ﻭﺍﻟﺮﺳﻎ
ﻭﺍﻟﺴﺎﻋﺪ؛ ﻻﻧﻪ ﻗﺪ ﺛﺒﺖ ﻋﻦ ﺍﻟﻨﺒﻲ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ
ﻭﺳﻠﻢ ﻣﻦ ﺣﺪﻳﺚ ﺳﻬﻞ ﺑﻦ ﺳﻌﺪ، ﻭﻭﺍﺋﻞ ﺑﻦ ﺣﺠﺮ،
ﻭﻫﻠﺐ ﺍﻟﻄﺎﺋﻲ ﻣﺎ ﻳﺪﻝ ﻋﻠﻰ ﺫﻟﻚ. ﺍﻣﺎ ﺍﻹﺭﺳﺎﻝ ﻓﻼ
ﺩﻟﻴﻞ ﻋﻠﻴﻪ، ﺑﻞ ﻫﻮ ﺧﻼﻑ ﺍﻟﺴﻨﺔ)).
Ma’ana: ((Wannan makruhi ne,
abin da yake Sunnah: Taro su da
sanya su a kan kirji, da kuma
sanya dama a kan tafin hagu da
wuyan hannu, da dantse, saboda
ya tabbata daga Annabi mai tsira
da amincin Allah daga hadithin
Sahl Dan Sa’ad, da Waa’il Dan
Hujur, da Hulb Attaa’ii abin da yake
nuna hakan. Amma sake hannaye
babu wani dalil a kansa, kai a
gaskiya ma shi sabanin Sunnah
ne)).
(5) Idan wani ya ce: Ko a cikin
shugabannin Mazhabar Imam
Malik akwai wadanda ke ganin
cewa da zarar an samu wata
fatawa a cikin Mazhabar
malikiyyah wacce ta saba wa
sahihiyar sunnar Manzon Allah, to,
a yi watsi da ita, a koma a yi riko
da sahihiyar sunnar Manzon Allah
mai tsira da amincin Allah kawai?
Amsa a nan ita ce: Lalle akwai su
da yawa, a gaskiya ma ni babu
wani shahararre daga cikinsu da
na sani yake cewa: Bayan
Bamalike ya fahimci cewa
sahihiyar Sunnah ta saba wa
malikancinsa ya yi watsi da
sahihiyar Sunnar ya cigaba da yin
aiki da abin da ya zo cikin
mazhabarsa kawai!! Ni ban san
wani mash’huri da ya fidi irin
wannan magana mara kan gado
ba. Gaskiyan lamari shi ne: Abin
da shugabannin mazhaba suke
cewa shi ne: Duk lokacin da wani
kaulin mazhaba ya yi karo da
sahihiyar Sunnah to sai a jingine
mazhabar a yi aiki da sahihiyar
Sunnah. Imam Malik da kansa
yana cewa kamar yadda ya zo
cikin littafin Tartiibul Madaarik
1/182:-
(( ﺍﻧﻤﺎ ﺍﻧﺎ ﺑﺸﺮ ﺃﺧﻄﺊ ﻭﺃﺻﻴﺐ، ﻓﺎﻧﻈﺮﻭﺍ ﻓﻲ ﺭﺃﻳﻲ
ﻓﻜﻞ ﻣﺎ ﻭﺍﻓﻖ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ ﻓﺨﺬﻭﻩ، ﻭﻛﻞ ﻣﺎ ﻟﻢ
ﻳﻮﺍﻓﻖ ﺍﻟﻜﺘﺎﺏ ﻭﺍﻟﺴﻨﺔ ﻓﺎﺗﺮﻛﻮﻩ )).
Ma’ana: ((Ni ba kowa ba ne face
mutum, ina yin kure kuma ina yin
daidai, sai ku rika yin nazari cikin
ijtihadina, dukkan abin da ya dace
da Alkur’ani da Sunnah sai ku rike
shi, kuma dukkan abin da bai dace
da Alkur’ani da Sunnah ba sai ku
bar shi)).
Sannan babban malami Jamaalud
Dinil Qaasimii ya ce cikin littafinsa:
Attahdiithu Fi Fununi Mustalahil
Hadith shafi na 245, da babban
malami Saalih Bin Muhammad
Alfullaanii cikin littafinsa: Iiqaazu
Himami Ulil Absar shafi na 89:
dukkansu biyun sun ce: Babban
malami cikin mazhabar Malikiyyah
Muhammad Almaqqarii ya ce cikin
littafinsa na Qwa’idul Fiqhi:-
(( ﻻ ﻳﺠﻮﺯ ﺍﺗﺒﺎﻉ ﻇﺎﻫﺮ ﻧﺺ ﺍﻻﻣﺎﻡ ﻣﻊ ﻣﺨﺎﻟﻔﺘﻪ
ﻷﺻﻮﻝ ﺍﻟﺸﺮﻳﻌﺔ ﻋﻨﺪ ﺣﺬﺍﻕ ﺍﻟﺸﻴﻮﺥ. ﻗﺎﻝ ﺍﻟﺒﺎﺟﻲ :
ﻻ ﺍﻋﻠﻢ ﻗﻮﻻ ﺍﺷﺪ ﺧﻼﻓﺎ ﻋﻠﻰ ﻣﺎﻟﻚ ﻣﻦ ﺍﻫﻞ
ﺍﻻﻧﺪﻟﺲ؛ ﻻﻥ ﻣﺎﻟﻜﺎ ﻻ ﻳﺠﻴﺰ ﺗﻘﻠﻴﺪ ﺍﻟﺮﻭﺍﺓ ﻋﻨﻪ ﻋﻨﺪ
ﻣﺨﺎﻟﻔﺘﻬﻢ ﺍﻷﺻﻮﻝ ﻭﻫﻢ ﻻ ﻳﻌﺘﻤﺪﻭﻥ ﻋﻠﻰ ﺫﻟﻚ.
ﺍﻧﺘﻬﻰ. ﻭﻗﺎﻝ ﺃﻳﻀﺎ: ﻗﺎﻋﺪﺓ: ﻻ ﻳﺠﻮﺯ ﺭﺩ ﺍﻷﺣﺎﺩﻳﺚ
ﺍﻟﻰ ﺍﻟﻤﺬﻫﺐ ﻋﻠﻰ ﻭﺟﻪ ﻳﻨﻘﺺ ﻣﻦ ﺑﻬﺠﺘﻬﺎ ﻭﻳﺬﻫﺐ
ﺑﺎﻟﺜﻘﺔ ﺑﻈﺎﻫﺮﻫﺎ؛ ﻓﺎﻥ ﺫﻟﻚ ﻓﺴﺎﺩ ﻟﻬﺎ ﻭﺣﻂ ﻣﻦ
ﻣﻨﺰﻟﺘﻨﺎ، ﻻ ﺍﺻﻠﺢ ﺍﻟﻠﻪ ﺍﻟﻤﺬﻫﺐ ﻟﻔﺴﺎﺩﻫﺎ، ﻭﻻ ﺭﻓﻌﻬﺎ
ﺑﺨﻔﺾ ﺩﺭﺟﺎﺗﻬﺎ، ﻓﻜﻞ ﻛﻼﻡ ﻳﺆﺧﺬ ﻣﻨﻪ ﻭﻳﺮﺩ ﺍﻻ ﻣﺎ
ﺻﺢ ﻟﻨﺎ ﻋﻦ ﻣﺤﻤﺪ ﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻴﻪ ﻭﺳﻠﻢ، ﺑﻞ ﻻ
ﻳﺠﻮﺯ ﺍﻟﺮﺩ ﻣﻄﻠﻘﺎ؛ ﻻﻥ ﺍﻟﻮﺍﺟﺐ ﺍﻥ ﺗﺮﺩ ﺍﻟﻤﺬﺍﻫﺐ
ﺍﻟﻴﻬﺎ )).
Ma’ana: ((Bai halatta bin zahirin
nassin Imami tare da sabawarsa
ga jigogin Shari’ah (Qur’ani da
Hadithi) a wurin korarrun
Shaihunai. (Imam) Baajii ya ce:
Ban san wani kauli da ya fi
tsananin saba wa Malik ba kamar
(kaulin) mutanen Andulus ba,
saboda Malik ba ya halattar da bin
masu ruwaya daga gare shi ba a
lokacin da suka saba wa Jigogi, su
ba sa dogara a kan haka. Intaha.
Sannan (Imam Baajii) ya sake
cewa: Qaa’idah: Bai halatta a yi
raddin Hadithai zuwa ga mazhaba
ta fiskar da zai rage wani abu na
armashinsu, kuma ya tafiyar da
amincewa da zahirinsu, domin
hakan bata su ne da kuma
wulakanta matsayinsu. Kada Allah
Ya kyautata mazhabobi ta hanyar
bacinsu (watau su hadithan) kada
(Allah Ya daukaka mazhabobin) ta
hanyar karya darajarsu (su
hadithan). Dukkan wata magana
Ana iya aiki da ita, ana kuma iya
yin watsi da ita, amma banda abin
da ya inganta a wurinmu daga
Muhammad mai tsira da amincin
Allah, ko kadan bai halatta a yi
raddin (maganarsa), domin abin da
ke wajibi shi ne: Yin raddin
mazhabobi zuwa gare ta)) (watau
maganar Annabi mai tsira da
amincin Allah).
(6) Idan wani ya ce: Dalilan nan
duka da ka kawo na cewa: dora
dama a kan hagu cikin salla shi ne
Sunnah, sake hannaye kuwa
sabanin Sunnah ne, wasu mutane
za su ce ba su gamsu da su ba,
hasali ma za su ce dukkan
hadithan masu rauni ne, saboda
haka yin salla hannaye a sake shi
ne daidai domin shi ne abin da
suka sani a mazhabar Malikiyya!!!
To, sai a ce da shi: Na farko dai da
ma ba dukkan gaskiyar da masu
wa’azi ke fada ba ne mutane ke
karba, Annabawa da Manzanni
sun gaya wa jama’arsu gaskiya,
amma an samu mutane da yawa
wadanda suka karyata su, suka yi
watsi da gaskiyar da suka fada
musu. Wannan shi ya sa za ka ga
‘yan bidi’ah da yawa suna karyata
ingantattun hadithan Buhari da
Muslim suka ruwaito cikin
sahihansu, matukar dai hadithan
sun saba wa abin da Dagutansu
suka dora su a kan shi iyazan
billah!
A bu na biyu shi ne: Ciwon son
zuciya na da wahalar waraka,
wannan shi ya sa duk yadda masu
wa’azi suka yi kokarin fahimtar da
Kiristoci cewa aqidarsu ta cewa
Allah yana da Da watau Isa, kuma
shi Allah Dayan uku ne! watau: shi
ne Allah Uba, sannan kuma akwai
Allah Da! Sannan kuma akwai
Allah Ruhu Mai tsarki! Duk lokacin
da masu wa’azi suka yi kokarin
fahimtar da su cewa wannan kure
ne bayyananne sai ka ga cewa
suna ta kawo tawilce-tawilce da
wasu shubuhohi domin tabbatar da
ra’ayinsu marar makama da hujja!!
Haka nan in ka dubi yan bidi’ah
nau’i daban-daban da ake da su
cikin Al’ummar Musulmi za ka rika
ganin yadda suke zaburowa da
karfi suna kare son zuciyarsu.
Misali yanzu in ka yi kokarin
fahimtar da batijjane cewa:
aqidarsa ta cewa Salatul Fatihi
saudaya tana daidai da Alkur’ani
sau dari shida wanda wannan
yana nufin ke nan Salatul Fatihi ta
fi Alkur’ani sau dari biyar da casa’in
da tara!! In ka shaida musu cewa
wannan akidah tasu wani nau’i ne
na ilhadi da raina Littafin Allah
Madaukakin Sarki, to nan da nan
za ka ga cewa sun yi ca a kanka
da zage-zage, da bace-bace, kuma
za ka ga cewa sun nace suna ta
yin tawilce-tawilce domin su
tabbatar da son zuciyarsa!!
To amma irin wannan hayaniya ta
yan bidi’ah, da ‘yan bin son zuciya
sam bai kamata ba a ce za ta hana
masu wa’azi ci gaba da shiryar da
Al’ummah zuwa ga sahihiyar
sunnar Annabi mai tsira da amincin
Allah ba.
Muna rokon Allah muna kaskantar
da kai a gabanSa da ya tausaya
Ya nuna mana gaskiya gaskiya ce
Ya ba mu ikon bin ta, Ya kuma
nuna mana karya karya ce Ya ba
mu ikon guje mata. Ameen.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

2 responses to “DORA DAMA A KAN HAGU CIKIN SALLA SHI NE SUNNAH, SAKIN HANNAYE CIKIN SALLA SABANIN SUNNAH NE(Dr Ibrahim Jalo Jalingo)”
  1. Albany Dabai Avatar
    Albany Dabai

    JazaakumulLAHU Khayran…

  2. […] DORA DAMA A KAN HAGU CIKINSALLA SHI NE SUNNAH, SAKINHANNAYE CIKIN SALLASABANIN SUNNAH NE(Dr Ibrahim …. […]

Leave a Reply to Albany DabaiCancel reply

Latest updates
Categories