Fatawoyin Rahama by Dr. Muhammad Sani Umar 2nd October 2022

Danna nan domin shiga group na karatu Online

  1. Ya hallata mutum ya ɗauke mahaifiyar sa da take aure a ƙauye zuwa inda yake zama a birni da izinin mijinta?
  2. Wanda ya karɓi aron kudi yayi noma amma abin da ya rage bayan ya biya bashi da bai isa yayi zakka ba- shikenan zakkar ta faɗi a kansa?
  3. Ya hallata ma’aikacin Kotu ya karɓi kuɗi da ake bayarwa in an raba gado ko wani abu makamancin haka?
  4. Menene ingancin maganar dake cikin littafin Ƙawaidi cewa duk wanda bai san ma’anar kalmar Shahada ba a cin yankansa, limancinsa da shaidarsa ba sa inganta?
  5. Hukuncin haɗiye kaki ga mai azumi?
  6. Ya hallata a ƙona Mushafin Al-ƙur’anin da ya lalace ko ya koɗe?
  7. Ya hallata amfani da Sabulu mai kumfa domin wankan tsarki/ibada?
  8. Ya hallata Miji ya umurci matarsa ta je gida ta huta in sun samu saɓani?
  9. Idan matar mutum ta yi tafiya a kwanar ta dole sai Mijinta ya cigaba da kwana a ɗakinta ko da yana da wata mata ba zai iya zuwa mata ba?
  10. Ya hallata mutum ya cigaba da yi wa mutane sallama ko da suna amsa masa da ‘ Yawwa’
  11. Idan makwabci yana cutuwa da makwabci saboda gidan kaji da yayi – makwabci dake cutuwa yana da wani haƙƙi?
  12. Ya inganta karanta Suratul Mulk kafin mutum ya kwanta bacci?
  13. Ya hallata idan mutum ya gama kiran sallah ba wutar lantarki sai aka dawo da wutar zai iya sake kiran sallah da lasfika !
  14. Menene hukuncin mutum mai zubar da ciki?
  15. Ya hallata likita ya yi Inshora a ƙasar da ake ɗaurawa likitoci alhakin biyar diyya ga marasa lafiya da suka rasa rayukansu sobada wani sakaci!
  16. Mutum zai iya zuwa kan ƙabari yayi Sallah ga wanda aka binne idan bayanan lokacin da aka yi masa sallar Jana’iza?
  17. Mutum zai iya kashe kyanwa da take masa ɓarna?
  18. Mutum zai iya sallar dare yana sunkuyawa yana ɗauka da ajiye Al-ƙur’ani?
  19. Ya hallata mutum ya tafi wata ƙasa wata shida ba tare da iyalansa ba?
  20. Ya hallata Liman yayi magana yana tsaka da Sallah in yana kokwonto sallar ta cika ko bata cika ba?
  21. Ya hallata mutum ya ƙi Rera karatu a Sallah saboda gudun riya!
  22. Shin akwai hujjar da ke nuna ajiye Al-ƙur’ani a ƙasa rashin girmama Al-ƙur’ani ne?
  23. Ya hallata mutum ya gina rijiya domin ladan ya riski iyayensa da sauran ‘yan uwansa da suka mutu!
  24. Idan mutum ya mutu yana zuwa wajen boka za a iya cin gadonsa?

Download
Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories