Fifita yardar Allah akan yardar waninsa

Domin neman ƙarin bayani danna nan

Maqala

Wanda ya nemi Yardar Allah koda ko hakan zai janyo masa Fushin mutane toh Allah zai wadatar dashi ga barin mutane ya kuma kare shi daga sharrinsu.

Wanda kuma ya nemi yardar mutane koda ko zai janyo fushin Allah, Allah zai barshi da mutane Kuma babu ruwanshi dashi.

Abinda Musulmi ya kamata ya lura dashi a rayuwarsa kullun shine neman yardar Allah ba yardar mutane ba, domin zuƙatan mutane a hannun Allah suke, idan Allah ya yarda dakai sai ya faɗa wa Mala’ikunsa a sama suma sai su soka, haka nan kuma a ban ƙasa ma mutane sai su soka. Amma in ka nemi yardar mutane har abada kana cikin baƙin ciki domin mutane bazasu taɓa yarda da kai ba har abada. Duk abinda kayi musu na alheri sai ka samu mai sukanka.

Allah yasa mudace.

Leave a Reply

Latest updates
Categories