GUJEWA HARAM DON KADA ZUCIYARKA TAKI HALAL(Sheikh Zakariyya Hassan Yakub)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

YANA KYAMATAR MATANSA
NA AURE. ko meye dalili?
Wani bawan Allah ne ya kai korafinsa
ga wani malami, akan cewa ya auri
matarsa, shekaru kadan da suke wuce,
yana da yara biyu da ita, amma akoda
yaushe sai ya rika ganin tana dada
muni a idonsa, kuma baya sonta cikin
zuciyarsa.
sai malamin ya tambayeshi, matar
naka tayi qibace sosai, sai yace a’a,
tayi hasarine da ya sanja halittarta? sai
yace a’a, halayenta basu da kyau ne?
yace a’a, sai malamin yace, amma kana
yawan kallon mata ko? sai yace ey,
kana kallon finafinai na batsa ko? yace
ey, sai malamin yace dole haka ya
kasance, domin duk lokacin da zuciya
ta saba da haram, idan mutum yana cin
haram ya sha haram, ya kwanta a
haram toh dole ya kyamaci halal, don
haka mu guje wa haram don jin dadin
halal. Allah yasa mu dace.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories