Kyakkyawan Mafarki Daga Allah Ne, Mummuna Kuma Daga Shaidan Ne.

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Assalamu Alaikum Warahmatullah wabarkaatuh.
Shin meye Hukuncin Mafarki da mukeyi a bacci, wani kyakkyawa mai faranta rai wani kuma mummuna mai bakanta rai?



Wasu zaka samu insukayi mafarki mara kyau toh sai kaga sun sanya kansu cikin damuwa da tashin hankali su rinka ganin kaman abinda suka gani a bacci gaskiya ne kuma zai faru dasu, wasu hakan tana sa har zargi ta shiga tsakaninsu da iyalansu su rinka ganin kaman suna aikata alfasha sabida kawai abinda suka gani acikin bacci.
Toh meye Hukuncin Mafarki Mai Kyau?
Duk wanda yayi mafarki mai kyau Mai faranta rai toh ya godewa Allah, kuma yana da daman ya sanar da na kusa dashi, domin wannan mafarki daga Allah take,
Abu Sa’eed(Radiyallahu anhu) Ya rawaito hadisi daga manzon Allah(sallallahu alaihi wasallam) Annabi yace: “idan dayanku yaga mafarki wanda yakeso, toh ya godewa Allah sannan ya bada labarin wannan mafarkin”
Bukhari Ya rawaito.
Haka nan a wata riwaya ta bukhari
Manzon Allah(Sallallahu alaihi wasallam) yace: “kyakkyawan mafarki daga Allah ne”
Abinda ya dace mutum yayi in yaga mafarki mai kyau:
Idan mutum yaga mafarki mai kyau acikin baccinsa toh bayan ya tashi sai yayi wa Allah godiya akan wannan mafarki yana mai fatan Allah ya tabbatar da ita,
Sannan kuma sai ya sanar da nakusa dashi.
Hukuncin ganin mummunan mafarki
Wanda duk yayi Mafarki mummuna, toh Kada ya daukesa da wani mahimmanci ballanta har ya gina wani Hukunci akansa, domin wannan daga shaidan ne.
An rawaito daga manzon Allah(sallallahu alaihi wasallam) yace: “Mummunan mafarki daga shaidan ne,duk wanda yayi mafarkin abinda yake tsoro toh ya nemi tsari daga Allah sannan yayi tofi a gefen hagunsa,sharrin wannan mafarki bazata cutar dashi ba” Albukhari.
A wata riwaya kuma:
“Idan mutum yaga mummunnan mafarki wanda bayaso, toh ya nemi tsari daga Allah, sannan Kada ya sanar da kowa shi.”
Abinda mutum zaiyi idan yaga mummunan mafarki:
Ya nemi tsari daga Allah daga shaidan.
Yayi tofi a gefen hagunsa sannan ya canza gefen da yake kwance akai.
Sannan inso samu ne ya tashi yayi nafila raka’a biyu.
Sannan kada yabaiwa kowa labari kuma kada ya damu kansa ko kuma ya kullace wani a dalilin wannan mafarki.
Daga Karshe akwai wani Bangare mai kama da mafarki amma ba mafarki bane, shi ana kiransa zancen zuci. Shine mutum zai sanya wani abu a ransa kyakkyawa ko mummuna yayi ta tunaninsa toh inyazo acikin baccinsa ma sai wannan abu yayi ta zuwa masa, toh itama wannan ba’a daukan ta komai ba’a kuma yin la’akari da ita.
Allah ya sa mudace. Wassalamu Alaikum.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

5 responses to “Kyakkyawan Mafarki Daga Allah Ne, Mummuna Kuma Daga Shaidan Ne.”
  1. aminu Avatar

    Allah ya saka da mafificin alkharin sa’ ameen.

  2. Rafiat Avatar
    Rafiat

    Allah yasaka d alkhairi

  3. Auwalu s.fulani kn Avatar
    Auwalu s.fulani kn

    Allah ya taimaka

  4. Mukhtar Darki Avatar
    Mukhtar Darki

    Allah ya saka da alheri

  5. Yusuf Ismail mamza Avatar

    Jazakallah khair

Leave a Reply

Latest updates
Categories