'YAN TIJJANIYYAH DA CIN MUTUNCIN ALLAH DA MANZONSA

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Bismillahirrahmanirraheem.
Yau inaso in share din wani sauti ne wanda wasu ‘yan tijjaniyyah suka zagi Allah da manzonsa acikinsa, wannan ya faru ne kaman yanda na sami labari awurin wani mauludin inyass. Inda suke nuna cewa shi inyass ya wuce gabar kowa, da dai kalamai munana na shirka da kafirci da fitsaranci.Kaman yanda kowa ya sani ne maluman Ahlussunnah sunyi kokari kuma suna kai wurin wayar da kan al’ummah akan tafarkin sufaye wanda wannan tafarki gurbatacciyace kuma Tana kaiwa ga halaka. Amma wani lokaci in ana bayanin hakikanin sufanci da abinda ta kunsa sai mutane su rika ganin kaman sharri ake musu, hatta wa’inda suke bin wannan tafarki ta sufancin sai surinka ganin abin karyane tsagoronta sabida su ba’a fada musu ainihin haqiqanin abin ba, su anrudesu ne dason annabi da kuma zikiri da salatin annabi, wanda ahakikanin lamari ba haka abin take ba. Amma yanzu ansami wanda suka yunkura daga cikin mabiya wannan tafarkin sufanci sukaje suka karanto hakikanin lamarin kuma suka dawo suna bayyana wa mutane gaskiyarta bawai don suka da bayyana aibinta ba, a’a don nuna wa mutane haqiqa subi. Daga cikin wa’innan wa’inda suka karanci haqiqanin lamarin ne aka sami wasu ‘yan darikar tijjaniyya suka fada kadan daga cikin aqeedarsu, hakan yakai ga wasu ‘yan tijjaniyyar sukayi Allah wadai dasu kuma suka nuna su basu tare dasu.
Toh haqiqanin gaskiya ‘yan’uwa wannan irin aqeedunsu kenan dama ga duk wanda ya sani, yana nan rubuce cikin littafansu. Saboda haka in kaji wani dan tijjaniyya yace ba haka bane toh bai karanci tafarkin bane, yana tafiyane a kife. Muna rokon Allah ya shiryar damu ya nuna mana gaskiya ya bamu daman binta, ya nuna mana karya ya bamu daman kauce mata.
DANNA NAN domin saukar da sautin. Wassalam
Mai Rubutu:
Nibras Muhammad Auwal.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

8 responses to “'YAN TIJJANIYYAH DA CIN MUTUNCIN ALLAH DA MANZONSA”
  1. nazifirabiua Avatar

    Reblogged this on nazifirabiua's Blog.

  2. kamaladdeen tukur funtua Avatar
    kamaladdeen tukur funtua

    Allah ka kara tsare mana imanin mu ya kuma tabbatar damu akan sunnah

    1. Ousmane arleeyou Avatar

      To Allah ka barmu da ingan taccen imani amin

  3. Aliyu Tijjani Avatar

    Wadannan Jabun yan Tijjaniyya ne. Kuma kowne fage akwai Baragurbi.

  4. Aliyu Tijjani Avatar

    Ya kamata a yi adalci ba dukan yan Tijjaniyya ne suke da wannan mummunan halinba, kamar yadda yake ba duka yan Izalane suke yan Boko haram ba. Ayi adalci.!!!

  5. Kabiru adamu Avatar
    Kabiru adamu

    Dan ALLAH DA MANZONSA S.A.W. akeyiwa yan tijjaniya adalchi wallahi ba haka bane hakikanin tijjaniyaba, babu inda babara gurbi akowace hanyakake, dan ALLAH miyiwa juna adalchi. Almusulumu akul musulum.

  6. HASBUNALLAHU WANI’IMAL WAKIL WA NI IMALMAULA WA NI IMANNASIR

  7. Duk mutumin dayace maka shi dan tijjaniya ne kuma yayi abinda kace wadancan mutanen sun aikata wlh qarya ne badan dariqa bane.

Leave a Reply

Latest updates
Categories