Nigeria sai Allah, kada mu maimaita kuskuren mu a zaben Nigeria ta 2023

Danna nan domin shiga group na karatu Online

An Fara ƙada gangar siyasar shekara ta 2023 a Nigeria, Dukkan ƴan takarar shugaban ƙasa sunyi harama, kowa yayi ɗamara, yana kai komo don ganin ya lashe zaɓe mai zuwa, yana tallata kansa, yana baje kolin hajarsa don samun masu saya.

Ya rage ga mu talakawa mu tantatance, mu duba wadda yafi gwanda gwanda acikin Wa’innan ƴan takara sai mu zaɓe shi.

Abinda yasa nayi wannnan rubutu shine don

jan Hankali kan kuskure da muka tafka a baya, ta yadda muka mance da Allah, muka ƙi neman zaɓin sa, muka Ayyana ɗaya daga cikin masu takara muka ce dole sai shi, shine kaɗai zai iya kawo mana gyara a ƙasa.

da yawa daga cikin mu hankulan mu ya kau saboda hali da ƙasar mu take ciki a wancan lokaci, da yawa daga cikin mutane suna ga babu wani wanda zai iya fitar da ƙasar daga Halin da take ciki sai wane. Sun mance da Allah.

Bazan mance a lokacin wannan zaɓe na taɓa faɗa wa wani aboki na cewa Allah ya zaɓa mana alheri tsaƙanin wa’innan ƴan takara, ya buɗi baki yace ai wane ne shine alherin, babu wani alheri in ba shi ba, nayi ƙoƙarin na fahimtar dashi kan cewa ba haka lamarin yake ba, zai yiwu kaso abu amma kuma ba alheri bane, zai yiwu ka ƙi abu ya zamo shine alherin kamar yadda Allah ya faɗa acikin Suratul Baqara ayah ta 216. Amma duk da haka bai yarda ba.

Kuma da yawa daga cikin mutane a wancan lokaci suna da irin wannan fahimtar, duk da cewa kuskure ne amma ni ina yi musu uzuri. Allah ya yafe musu damu baki ɗaya.

a tunani na wannan mancewa da Allah da mukayi muka dogara da wani wanda bashi ba yana daga cikin sabbuban da Allah ya jarrabe mu domin mu koma cikin hankulan mu, mu sake tunani, mu gane cewa Allah shi kaɗai ne yake yaye Musiba ba wani ba.

Saboda haka ga nan zaɓe na Shekarar 2023 na zuwa, Kada mu sake yin wannan kuskure, Babu faɗa kan wani ɗan takara, mu duba wanda muke ga zai kamanta gaskiya, mu zaɓe shi, sannan mu mayar da lamarin mu zuwa wurin Allah, mu roƙe shi ya taimaka masa wurin yin abinda ya dace.

domin zuƙatan bayi a hannun Allah suke, wanda kake masa tunanin shine na ƙwarai zai iya juya wa, haka nan wanda kake masa tunanin shine na banza Allah kan iya canza zuciyarsa yayi aiki na gari.

Muji tsoron Allah, Mu koma zuwa gareshi, mu roƙe shi ya nuna mana ɗan takara da ya dace mu zaɓa, kada mu bari Son zuciya ta ɗebe mu mu mance da Allah muce sai Wane sai wane. Muce sai Allah. Allah ne kawai zai iya Fitar damu daga halin da muke ciki.

Allah mun tuba ka kawo mana ɗauki, ka zaɓa mana Shuwagabanni na gari.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories