Yadda zakayi lissafin Zakkan ka da yadda zaka cire da wadda ake basu

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Zakka wajibi ne akan kowani Musulmi wanda dukiyarsa ta kai Nisabi. Yana daga cikin Rukunan Musulunci guda biyar. Duk wanda Allah ya hore masa dukiyar da takai Nisabi to dole ya cire wannnan kaso da Allah ya ɗora masa, ya baiwa wa’inda Akace a basu.

Su waye ake basu Zakka?

  • Talakawa
  • Miskinai
  • Masu aikin tattara Zakka
  • Wanda ake Jan ran su zuwa ga Addinin Musulunci
  • Ƴanta bayi
  • Wanda ake binsu bashi
  • Ɗaukan nauyin jihadi
  • Matafiyi da guzurinsa ya ƙare

Wa’innan sune ake basu Zakka kamar yadda Allah yayi bayani acikin Surat-Taubah aya ta 60.

Akwai Nisabi da dukiya sai ya kai kafin a cire masa Zakkah, a wannan Rubutu zamuyi magana ne kan zakkar Kuɗi.

Hanya mafi sauƙi domin sanin Nisabin Zakkah a Nigeria shine a binciki Shafin komitin Ganin wata ta ƙasa. Domin shi Nisabin yana canza wa lokaci zuwa lokaci gwargwadon tashiwar farashin zinari da kuma ƙarfin Naira. Saboda haka yasa wannan Komiti suna Rubuta duk wani canji da aka samu game da nisabin Zakka.

Ƙarshen Rubutu da sukayi na Nisabin Zakkah Ranar 23 ga watar December 2022 ya nuna cewa Nisabin Zakka yana ₦2,196,000(Miliyan Biyu da dubu ɗari ɗaya da casa’in da shida). Idan mutum dukiyar sa ta kai wannan kuma shekara ya kewayo akan wannan dukiya to zai cire mata zakka.

Misali mutum kuɗinsa ta kai miliyan uku kuma shekara ta juyo wannan dukiya tana nan yaya mutum zai cire wa wannan dukiya zakka?

Hanya mafi sauƙi shine ya kasa kuɗin gida arba’in sai ya cire kashi ɗaya wannan Shine rabon Allah. Lissafin zai zama kaman haka(3,000,000/40=75,000) anan abinda zai cire wa naira miliyan uku shine dubu saba’in da biyar(75,000).

Kamar yadda nayi bayani a baya musani cewa Nisabi yana canza wa lokaci zuwa lokaci. Saboda haka duk lokacin da zamu cire zakkah to mu bincika musan nawa ne nisabi a wannan lokaci. Sannan mu sani ba da zaran kuɗin mutum ya kai nisabi zai cire zakkah ba. A’a sai shekara ta kewayo akan dukiyar tukunna.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories