TAKAITACCEN TSOKACI A KAN JAWABIN SHEIK DAHIRU BAUCHI(Dr. Ibrahim Jalo Jalingo)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Jawabin da Malam Dahiru
Bauchi ya yi a shirin safe na BBC
hausa a yau 21/5/2015, hakika
ya fadi daidai cikin wani sashi
nasa, ya kuma kasa fadin daidai
cikin wani sashi nasa.Ya fadi daidai a inda ya kafirta
‘yan Tijjaniyyar nan da suka yi
bukin maulidin Sheik Ibrahim
Inyas a garin Kano, sannan a
wajen wannan buki nasa
wasunsu suka yi ta furta
kalaman batunci ga Annabi Mai
tsira da amincin Allah.
Amma bai fadi daidai ba a inda
ya ce babu abin da ake kira Ahlul
Hakikati cikin Darikar Tijjaniyyah,
ya kuma fadi hakan ne duk kuwa
da cewa a cikin Darikar tijjaniyyah
a kwai yarda da abin da ake kira
Wahdatul Wujudi, shi kuwa
Wahdatul Wujudi tabbas yana
daga cikin lazimin wannan akida
yarda da irin maganar cewa
Ibrahim Inyas Allah ne.
Ko shakka babu a cikin darikun
Sufaye musamman Darikar
Tijjaniyyah a kwai gurbatattun
akidu daban daban na tozarta
Alqur’ani, da tozarta Manzon
Allah mai tsira da amincin Allah,
da ma tozarta Zatin Allah shi
kanSa, hakika dukkan masu
nazarin littattafan wadannan
darikun sun san da haka.
To amma dai a takaice muna iya
cewa an dan samu ci gaba cikin
jawaban da shi Malam Dahiru
Bauchi ya yi; domin a da irin
wannan bayanin ne na bayyanar
da kafircin wasu akidu na Sufaye
idan Ahlus Sunnah masu
Da’awah suka bayyana su ga
Duniya zai a ji wasu daga cikin
masu gafala ko son zuciya suna
ta cewa: ‘Yan Izala na kafirta
Musulmi!
Muna fata Malaman Sufaye a ko
ina suke za su yi hakuri, su kara
tunani su sa tsoron Allah cikin
lamuransu su daure su yi
Musuluncin nan kamar yadda
Annabi Mai tsira da amincin
Allah tare da Sahabbansa suka yi
shi. Allah Ya taimake mu.
Ameen.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

18 responses to “TAKAITACCEN TSOKACI A KAN JAWABIN SHEIK DAHIRU BAUCHI(Dr. Ibrahim Jalo Jalingo)”
  1. Samaila Shiko Avatar
    Samaila Shiko

    Allah ya taimaki Mallam.

  2. kamaladdeen tukur funtua Avatar
    kamaladdeen tukur funtua

    Allah yasa dahiru bauchi yazama ahlus-sunnah cikakke

  3. Usman Avatar
    Usman

    Kaiko jalo makaryacine adarika wallahi bawasu yan hakika hasalima shehu yayi risalatul muntakimu jalon jahilai baamagana sai anyi bincike

  4. Assalamu alaikum jama’a ina tanbaya meyasa idan anayancen musulmai a nigeria ba’asa yan shi’a ne shinkosu ba musulmai bane???

  5. faruq Bayero Avatar
    faruq Bayero

    Malan Usman Ai ba fada bane kamar yanda malan jalo jalingo ya fadi hujjo Jin shi bai yi zagi ba hujjoji ya fada sai ka fadi hujjan ka kuma ka fadi littafin da ka dogara da shi kuma ka fadi shifin da yake kuma ka sani fa mai Abun fada baya fada Mara Abun fada shi yake fada Allah ya kara shiryadda mu Ameen

    1. Auwal.abdul.31 Avatar

      aikowa yasan yan,izal arnane kuma kafiraine kuma cinmatan mutane suke amasallahci kaiwawa dakake izala bakasan meyake faruwa kaje kai bincike akan izala kuma menene izala.inaso dan izala yaje yaibincike akan izala kafin yasan mene mah izalarma. mumun san maye sunnar tasu bawata bace illah fasukanci damatan mutane dan izalah kai badan sunnabane,saidai kace kai dan ahalil sunsunanekai shine zamu yarda dakai.idanko hakane to munyarda.dama kun ce akoyawa mata karatu agida kafircine ammah mutane sukawo matansu masallahci kucisu wannan sunnane kai yan,izahla wallahi kunji kunya.matsiyata sunannu iyalan fir auna da hamana.

  6. Sulaiman Adam Mai Kambu Avatar
    Sulaiman Adam Mai Kambu

    Hm haba jalo jalingo harkana da bakin magana anan kamanta Zagin da kayiwa syd Aliyu bin Abidalib kamanta zagin da Ibni taimiya yayiwa syd Nana Kadija da Syd Nana Fatsuma Acikin Littafinsa Minahaji sunnah Kamanta fatawawar sa akan ziyarar Annabi S.A.W.kumakamanta Gumi dayace yan Darika kafiraine ai ba yanhakika yaceba Amdayake Bakada Adalci kajimaganar da kakae fada

  7. Mudallab sani Avatar
    Mudallab sani

    Allah ya kara hada kan musulmin Nigeria dama duniya baki daya amin

  8. shamsi sani gumel Avatar
    shamsi sani gumel

    ya allah ka shiryar da yan hakika su fahimci sunna.

  9. Been umar Avatar
    Been umar

    Allah Yashirya yan izala idan sunada rabon shiriya a kullun basuda aiki sai karya da kafirta yan darika kuma kusani cewa wallahi yan darika sunfi karfinku makiya manzon Allah (SAW) kai Allah ya tsine maku Kuma da sannu duk sai Allah Ya halakar daku dakuda mabiyanku

  10. Hamza mustapha Avatar
    Hamza mustapha

    Allah yasa mugane gaskiya.

  11. Kamal Abdullahi Ali kura,kano state Avatar
    Kamal Abdullahi Ali kura,kano state

    Allah ya saka da alkhairi malam sulaiman adam sabo da tunatarwar da kaiwa wannan azzalumi,dan son zuciya wato jalo jalingo kan irin mummunar akidar su ta kin ahlulbaiti da kafirta masoyan shugaba(saw)wato yan darikun sufaye.Bayan haka kai kuma jalingo ka manta fadin Gumi cewa gara kirista da musulmi dan darika,da cewa jefa kuri’a yafi sallah?

  12. Dahiru Bako Avatar
    Dahiru Bako

    Ai kuwa Shehu Dahiru bauchi shine cikakken Ahlisunnah

  13. Nidai badan juyawa gaskiya bayaba,kuma badan daina bintaba har’abada. Darika itace hanya guda daya wacce zata tserataddamu daga halaka da fadawa rudin zamani.Muso Annabi Fiyeda kowa da komai, mu rike alkur’ani da hadisan annabi ingantattu.

  14. Isma'il safana Avatar
    Isma’il safana

    Mutane muji tsoron Allah

  15. Adamu babaji aliyu Avatar
    Adamu babaji aliyu

    To mudai mun riki son annabi da magabata musamman ma shehu ibrahim

  16. Abdallah abubakar jasawiy Avatar
    Abdallah abubakar jasawiy

    Subhanallah
    Wasu basa kunyan karya
    Tur’da wanda ke batanci ga sallihan bayi

  17. Abdallah abubakar shaukin yabo Avatar
    Abdallah abubakar shaukin yabo

    Shehunmu shiek dahoru bauchi
    Ba sa’anku bane
    Ko gun karatu kussani
    Munnamu mallamaine na gaskiya ba aikin kudi sukeyi ba ko contract
    Kai idan baka yardaba
    Munnada mallamai wanda idan dibet ce ta kama; hohoho za kugane babancin ayya da yayan borrisss
    Wai ku yan sunnah hmmm
    Saide yan nasir nana
    😣

Leave a Reply

Latest updates
Categories