FALALAR SAHABBAI( Sheikh Abdulwahhab Abdullah)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

Alhamdu lillahi rabbil A’lamin, wa
Sallallahu wa sallama ala Nabiyyina
Muhammadin Wa ala a’alihi wa
sahbihi ajma’in.
Amma ba’ad, hakika hadisi ya tabbata
daga Anas Bin Malik radhiyallahu
anhu ya ce;
ﻛﺎﻧﺖ ﺍﻷﻧﺼﺎﺭ ﻳﻮﻡ ﺍﻟﺨﻨﺪﻕ ﺗﻘﻮﻝ
ﻧﺤﻦ ﺍﻟﺬﻳﻦ ﺑﺎﻳﻌﻮﺍ ﻣﺤﻤﺪﺍ ﻋﻠﻰ ﺍﻟﺠﻬﺎﺩ ﻣﺎ ﺣﻴﻴﻨﺎ ﺃﺑﺪﺍ
ﻓﺄﺟﺎﺑﻬﻢ
ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻻ ﻋﻴﺶ ﺇﻻ ﻋﻴﺶ ﺍﻵﺧﺮﻩ ﻓﺄﻛﺮﻡ ﺍﻷﻧﺼﺎﺭ
ﻭﺍﻟﻤﻬﺎﺟﺮﻩ
Ma’ana
Ansar sun kasance a yayin da suke
haka ramin khandaku suna cewa;
“Mu ne wadanda suka yiwa Manzon
Allah sallallahu alaihi wa sallama
mubaya’a akan jihadi muddin muna
raye har abada”. Sai Manzon Allah
sallallahu alaihi wa sallama ya ce;
“Ya Ubangiji babu wata rayuwa sai
rayuwar lahira.
Ya Allah ka girmama Ansar da
muhajirai”
‘Yan uwa wannan ya nuna bai halatta
wani mutun ya zagi sahabbai wadan
suke kaunar Manzon Allah sallallahu
alaihi wa sallama shima yake
kaunarsu ba, duk wanda ku ka ji yana
zaginsu ku Sani wannan tababbe ne,
yayi asara duniya da lahira.
wa Sallallahu wa sallama ala
Nabiyyina Muhammadin Wa ala
a’alihi wa sahbihi ajma’in.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories