Idan mutum yana cikin yin sahur, sai ya ji kiran sallah yaya zai yi?( Sheikh Abdulwahhab Abdullah)

Danna nan domin shiga group na karatu Online

AMSA:
A irin wannan hali mutum zai
qarasa abin da ke hannunsa ne.
Domin hadisi ya tabbata daga Abu
Huraira radhiyallahu anhu ya ce:
Manzon Allah sallallahu alaihi wa
sallama ya ce:
ﺇِﺫَﺍ ﺳَﻤِﻊَ ﺃَﺣَﺪُﻛُﻢْ ﺍﻟﻨِّﺪَﺍﺀَ ﻭَﺍﻟْﺈِﻧَﺎﺀُ ﻋَﻠَﻰ ﻳَﺪِﻩِ ﻓَﻠَﺎ
ﻳَﻀَﻌْﻪُ ﺣَﺘَّﻰ ﻳَﻘْﻀِﻲَ ﺣَﺎﺟَﺘَﻪُ ﻣِﻨْﻪُ
Ma’ana:
Idan dayanku ya ji kiran sallah
alhali qwarya tana hannunsa, kada
ya ajiye ta, har sai ya biya
buqatarsa .
Amma a nan sai a yi hattara, kada
a mayar da irin wannan dabi`a ta
zama al`ada a kullum domin ba
ance mustahabbi bane yin hakan
ballantana a ce ana so a rinqa yi,
sassauci ne akayi ga wanda ya
fara cin abinci sai lokaci ya kure
masa.
wa sallallahu wa sallama ala
Nabiyyina Muhammadin wa ala
aa’lihi wa sahbihi ajma’in.

Donate

Bada gudunmawa domin Yada Addinin Musulunci
Account Number: 4568496377
Bank: Moniepoint
Name: Islam Online Archive

Leave a Reply

Latest updates
Categories